• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

AREWA: Sai Yawan Jama’a Ba Yawan Jami’a; Boko Ko Bokoko?

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
April 21, 2019
in Babban Labari, Rahotanni
0
Magautan Sarki Kano Muhammadu Sanusi II na fili da na boye

Alhaji Ahmadu Bello, premier of Northern Nigeria and Emir of Kano at the inauguration of Daily Mail ,Kano 1961

Cikin makon da ya gabata, jaridar Daily Trust ta buga yawan jami’o’i wadanda ba na gwamnati ba a fadin kasar nan. Sun yi dalla-dalla suka fayyace yawan jami’o’in da kowace Shiyyar Najeriya ta mallaka. Amma fa wadanda ba na gwamnati ba.

A nazari da PREMIUM TIMES HAUSA ta yi bisa wannan rahota na yadda Arewa ta zama koma-baya wajen kafa jami’o’i, domin samun ingantaccen ilmin matasan yankin. Shiyyoyin Kudu maso Kudu, Kudu maso Yamma da Kudu maso Gabas sun yi wa Arewa gaba dayan ta fintinkau wajen samar da wadataccen ilmin jami’a ga yaran da suke haihuwa.

Ilmin zamani, wanda a kasar Hausa farkon shigowar sa aka rika kira da sunan muzantawa, wata ilmin boko, ya shigo yankin Kudu masu Yamma a lokaci daya da shigowar addinin Kiristanci a Lagos, wajajen 1846.

SHIGOWAR ILMIN ZAMANI AREWA

An samu tazarar shekaru ba goma ba, ba talatin ko araba’in ba a tsakani, kafin ilmin zamani ya shigo Arewa. Lokacin da ya shigo din ma, ba a karbe shi hannu bibbiyu ba, sai aka kyamace shi kamar yadda ake kyamatar giya ko najasa.

Har sai da ta kai an rika kyamata da tsangwamar yaran da aka sa makarantun zamani a lokacin, wato ’yan makarkatar boko, maimakon ma a rika kiran su da ’yan makarantar boko.

Sannu a hankali kaka-gidan da Turawa suka yi a Arewa, bayan kifar da Daular Usumaniyya, sai karatun zamani ya fara karbuwa a Arewa, ko kuma a ce kasar Hausa, amma akasari a gidajen sarakunan gargajiya, hakimai da dagatai da sauran wadanda ke rabe da su.

Sai dai kuma an rika tilasta talakawa saka ‘ya’yan su makaranta ko da ba su so.

GUDUN KARATUN BOKO: ‘IYAR NISAN DAN KA, IYAR LADAR KA’

Wannan tilastawa da aka rika yi, ta haifar da gudun hijirar da iyaye suka yi da yaran su. Wato an rika dauke yara ana tafiya da su makarantun allo a garuruwa masu nisan gaske, da nufin tserewa daga kararun ‘Nasaranci’. Wato karatun boko.

A wancan lokacin an rika kyamatar karatun zamani matuka, har aka rika yi wa iyayen yara ‘fatawar-molon-ka’ cewa iyar nisan inda ka gudu da yaron ka, to iyar yawan ladar ka a wajen Allah.

Dalili kenan sai a dauki yaro daga Funtuwa ko Kankara a kai shi karatun allo Maiduguri ko Fataskum ko Gashuwa. Wasu kuma a lula Sakkwato da su ko Kano Kaura Namoda ko Zariya.

An rika yin gugumarar yin zugar kai yara karatun allo zuwa Maiduguri, har ta kai aka rika kiran Barno da sunan “Gabas”, kamar yadda ake kiran Makka da suna “Gabas.” Shi ya a lokacin idan wani ya tafi Makka, sai a ce ya tafi “Gabas, gaba da Gabas. Wato ya tafi gaba da Barno kenan.

Yawancin yaran da ake kai wa, ba su dawowa gida sai sun sauke Akur’ani. Wani a ranar da aka yi masa sauka za a yi masa aure, wani kuma sai shekara ta kewayo.

Da haka gidajen sarakai da na jikin su su ka rika yin zurfi a cikin karatun zamani, har suka rika fita Ingila, a daya gefen kuwa yaran jama’ar karkara na kara nausawa “Gabas” su na zuwa karatun allo.

A haka aka rika tafiya tsawon lokaci, Kudu na yi wa Arewa rata wajen karatu, su kuma gidajen sarautun gargajiya da makusantan su na yi wa sauran talakawan su tazara a karatun zamani.

ILMIN ZAMANI: AN DADE DA BARIN HAUSAWA BAYA –Ibramim Kurawa

A cikin wata hira ta musammnan da PREMIUM TIMES HAUSA ta yi da Dakta Ibrahim Kurawa, wani masanin tarihi a Kano, a cikin Agusta, 2017, ya bayyana yadda tun farko aka bar Arewa, a baya a fagen ilmin zamani. Ga abin da ya ke cewa:

“Batun ilmi da ka fara yi, idan ka kalli lamarin, za ka ga cewa shi dama Bahaushe tun cikin karni na 19 har zuwa lokacin da Turawan mulki su ka shigo, bai damu da neman ilmi ba. Kai dai bar shi ga noma da fatauci kawai. Yayin da su kuma Fulani su ne malamai, su kuma ke karatun sauran fannonin ilmin musulunci.

“Wannan sai ya bai wa Fulani damar karkata zuwa ga ilmin zamani lokacin da Turawa suka shigo. Dama kuma shi kan sa ilmin zamanin a kasar Hausa dai ai ta hannun sarakunan gargajiya ya shigo, wadanda Fulanin ne, su ke mulki.

“Turawan Mulki sun rika tilasta wa sarakuna da sauran masu mulkin gargajiya su sa ‘ya’yan su makarantar boko. Dalibin farko a makarantar Gidan Danhausa a Kano, Bafulatani ne, sauran ma duk Fulanin ne duk ‘ya’yan masu mulki. Kai ko a firamare ma duk ‘ya’yan sarakuna da masu mulki ne su ka fara shiga, ko aka fara dauka.

“To haka abin ya rika tafiya. Ka ga ashe duk wanda ya kammala karatu, shi ma a gaba zai sa na sa yaran. Wadanda ba su fara karatu ba a lokacin, to za a dauki lokaci mai tsawo kafin su cimma tazarar da aka yi musu.

“Bahaushen farko da ya fara karatu a Makarantar Middle ta Kano shi ne Musa Iliyasu, ina zato a cikin 1939 ko 1940 aka sa shi makarantar. Malam Aminu Kano ma ya riga shi shiga kenan, domin shi tun a wajajen 1936 ya shiga Makarantar Katsina. To sai ka duba da kyau, Bello Kano, Dokaji, Ahmadu Matidan, Sani Dan Ciroma duk sun riga Musa Iliyasu shiga da shekaru kusan 20. Domin su tun a 1921 or 1922 su ka shiga. Dukkan su kuma Fualani ne idan ka debe Matidan, wanda shi Balaraben Kano ne.

“Dalibin farko a Kwalejin Barewa ina jin a cikin 1923, mai suna Abubakar, Bafulatani ne daga Sokoto. Shi aka fara dauka a tarihin Kwalejin Barewa. Shi ne ma ya zama Madakin Sokoto daga baya. Dalibi na hudun dauka, Ahmadu Matidan ma dan Kano ne, amma Balarabe. Ahmadu Bello shi ne wanda ya fara zuwa Kwalejin Katsina daga cikin jinin Shehu Danfodiyo. Ina jin wajajen 1926. Da wannan ilmin ne Fulani su ka fara shiga gaban Hausawa wajen aikin gwamnati da kuma mulki na siyasa a tarihin Nijeriya.”

Inji Kurawa, wanda ya yi Daraktan Bincike da Tattara Bayanai a zamanin Gwamnatin Ibrahim Shekarau, a Jihar Kano.

Bayan kafa jami’o’i a Arewa, ilmin zamani ya samu tagomashin karbuwa ganin yadda aka karbi mulki a hannun Turawa, kuma dukkan al’amurran tafiyar da mulki, gudanarwarwa da gwamnati duk sun koma karkashin ’yan kasa.

Amma duk da haka, kudu ta yi wa Arewa fintinkau ko a lokacin, domin ta kasance yawanci ’yan kudu ne suka yi kaka-gida a kan mukamai da yawa a Arewa.

AREWA: GA JAMA’A AMMA BABU JAMI’A

A yau ba jiya ba kuma ba gobe ba, idan aka auna yawan jami’o’in da ba na gwamnati ba, wadanda aka kafa a kudancin kasar nan, za a ga cewa an yi wa Arewa fintinkau a fannin neman ilmin zamani.

Ba don an yi sa’a gwamnonin jam’iyyar PDP sun gina jami’o’i na Gwamnatin Jiha a jihohin su ba, to da tabarbarewar ilmin jami’a a Arewa ya yi muni sosai yanzu a Arewa.

Gwamnonin PDP sun kafa jami’ar Jiha a Katsina, Gombe, Jigawa, Kano, Kaduna da sauran Jihohi da dama a Arewa. Wannan ya kara yawan jami’o’i a Arewa, amma kuma babu yawan masu zaman kan su kamar kudancin kasar nan

KUDU NA JAMI’A AREWA NA JAMA’A

Kididdiga ta tabbatar da cewa a yanzu haka akwai jami’o’I masu zaman kan su wadanda ban a gwamnati ba a Yankin Kudu maso Yamma har guda 36. Jihohin Kudu maso Yamma su ne Lagos, Ogun, Ondo, Oshun, Ekiti.

A jihohin Kudu maso Kudu kuwa akwai jami’o’i wadanda ba na gwamnati ba har 14. Jihohin Kudu maso Kudu sun hada da Bayelsa, Rivers, Cross River, Akwa Ibom.

Yankin Kudu maso Gabas da ya kunshi Enugu, Anambra, Abia, Imo da Ebonyi, akwai jami’o’i da ba na gwamnati ba har 13.

Amma kakaf a fadin Yankin Arewa maso Yamma, wato jihohin Kano, Kaduna, Katsina, Zamfara, Sokoto, Kebbi da Jigawa, jami’a guda 3 ce rak ta masu zaman kan su.

Wannan yanki na Arewa maso Yamma shi ne ya fi yawan jama’a a Najeriya, yawan jama’a a Arewa, kuma shi ne ya fi samar da yawan kuri’u a zabe.

Arewa maso Gabas da ya hada da Gombe, Adamawa, Bauchi, Yobe da Barno, akwai jami’a 2 kacal.

Wannan yanki ne Boko Haram ya yi katuru, wanda ya samo tushen fitinar sa daga haramta karatun boko.

Yankin Arewa ta Tsakiya, da ya hada da FCT Abuja, Neja, Plateau, Benuwai, Nasarawa, Kwara, Kogi da Taraba, akwai jami’o’i masu zaman kan su guda 11.

Idan aka hada jimmila za a ga cewa a Arewa gaba daya akwai jami’o’i 16, su kuma Kudu akwai 63, duk masu zaman kan su, wadanda bana gwamnatin jiha ko na tarayya ba.

RASHIN JAMI’O’I A AREWA: Wani Babban Cikas

Baya ga tazarar da aka yi wa Arewa a jami’o’j masu zaman kan su, to wata babbar tazara kuma ita ce a addinance ma an yi wa musulmai tazara wajen kafa jami’o’i.

Wadannan jami’o’i na Kiristoci, ba fa addinin kiristancin zunzurutu suka koyarwa ba, sun a koyar da fannoninn ilmin zamani ne ne, kamar yadda sauran jami’o’in Gwamnatin Tarayya, na Jihohi da sauran na masu zaman kan su ke koyarwa.

Bincike ya nuna cewa akwai jami’o’i 32 mallakar manya-manyan coci-coci na kasar nan. Amma jami’o’i 2 ne rak mallakar kungiyoyin musulunci a nan kasar.

Sannan kuma baya ga jami’o’i 32 da coci-coci na Kiristoci suka mallaka, akwai ma wasu guda 15 a yanzu haka da wasu manyan coci-coci na kasar nan ke jira a ba su lasisi su kafa.

Karin tazara da aka yi wa Arewa wajen jami’a kuma ita ce jami’ar nan ta Gwamnatin Tarayya, wadda ake yin karatu daga gida, wato National Open University of Nigeria (NOUN).

Cikin watan Maris, 2019 ta yaye dalibai 20,799, amma kusan kashi 80 bisa 100 duk ‘yan kudu ne.

Sannan kuma ta na da dalibai sama da 400,000, amma kusan kashi 80 duk ‘yan kudu ne daliban. ’Yan Arewa ba su cika maida hankali wajen shiga jami’ar ba, sai cikin shekarun nan uku, bayan an bai wa Farfesa Abdalla Uba Adamu na Jami’ar Bayero ta Kano shugabancin jami’ar sannan aka karkato da hankulan ‘yan Arewa shiga jami’ar ta NOUN.

A karshe, cikin makon da ya gabata an bayyana cewa akwai jami’o’I 303 da ake son a yi wa rajista a kasar nan?

Shin nawa ne a cikin su za a kafa a Arewa? Kada fa mu Arewa ta shankake har sai Chana ta zo ta yi mana kaka-gida a fannin ilmi a Arewa, kamar yadda yadda suka yi kaka-gida a harkokin kasuwanci a Kano.

Tags: ABUAbujaBokoBUKHausajami'oiKaratuLabaraiNajeriyaNewsPREMIUM TIMESSokotoUDUZaria
Previous Post

HOTUNA: Yadda mazauna Unguwannin Kaduna suka yi zanga-zangar kira ga gwamnati da ta kawo karshen ayyukan mahara

Next Post

ILMIN ZAMANI: An dade da barin Hausawa a baya –Ibramim Kurawa

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
pupils_of_dukawiya_science_p.s_in_computer_class_gwale_lgea

ILMIN ZAMANI: An dade da barin Hausawa a baya –Ibramim Kurawa

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • SHARI’AR ZABEN SHUGABAN ƘASA: Kotu ta karɓi sakamakon zaɓen jihohi 17 daga hannun Peter Obi domin tantance sahihancin su
  • TSAKANIN ATIKU DA KEYAMO: Keyamo ya ɗaukaka ƙarar hukuncin tarar Naira Miliyan 10 da Kotun Tarayya ta danƙara masa
  • KOTUN ZAƁEN SHUGABAN ƘASA TA ƊAU ZAFI: Yadda Atiku ya kaɗa hantar Tinubu, APC da INEC a zaman shari’ar ranar Laraba
  • Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai
  • Sanatoci 67 sun rattaba hannu Yari suke so, da karin wasu na nan tafe – Inji Abdul Ningi

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.