• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

AREWA: Sai Yawan Jama’a Ba Yawan Jami’a; Boko Ko Bokoko?

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
April 21, 2019
in Babban Labari, Rahotanni
0
Magautan Sarki Kano Muhammadu Sanusi II na fili da na boye

Alhaji Ahmadu Bello, premier of Northern Nigeria and Emir of Kano at the inauguration of Daily Mail ,Kano 1961

Cikin makon da ya gabata, jaridar Daily Trust ta buga yawan jami’o’i wadanda ba na gwamnati ba a fadin kasar nan. Sun yi dalla-dalla suka fayyace yawan jami’o’in da kowace Shiyyar Najeriya ta mallaka. Amma fa wadanda ba na gwamnati ba.

A nazari da PREMIUM TIMES HAUSA ta yi bisa wannan rahota na yadda Arewa ta zama koma-baya wajen kafa jami’o’i, domin samun ingantaccen ilmin matasan yankin. Shiyyoyin Kudu maso Kudu, Kudu maso Yamma da Kudu maso Gabas sun yi wa Arewa gaba dayan ta fintinkau wajen samar da wadataccen ilmin jami’a ga yaran da suke haihuwa.

Ilmin zamani, wanda a kasar Hausa farkon shigowar sa aka rika kira da sunan muzantawa, wata ilmin boko, ya shigo yankin Kudu masu Yamma a lokaci daya da shigowar addinin Kiristanci a Lagos, wajajen 1846.

SHIGOWAR ILMIN ZAMANI AREWA

An samu tazarar shekaru ba goma ba, ba talatin ko araba’in ba a tsakani, kafin ilmin zamani ya shigo Arewa. Lokacin da ya shigo din ma, ba a karbe shi hannu bibbiyu ba, sai aka kyamace shi kamar yadda ake kyamatar giya ko najasa.

Har sai da ta kai an rika kyamata da tsangwamar yaran da aka sa makarantun zamani a lokacin, wato ’yan makarkatar boko, maimakon ma a rika kiran su da ’yan makarantar boko.

Sannu a hankali kaka-gidan da Turawa suka yi a Arewa, bayan kifar da Daular Usumaniyya, sai karatun zamani ya fara karbuwa a Arewa, ko kuma a ce kasar Hausa, amma akasari a gidajen sarakunan gargajiya, hakimai da dagatai da sauran wadanda ke rabe da su.

Sai dai kuma an rika tilasta talakawa saka ‘ya’yan su makaranta ko da ba su so.

GUDUN KARATUN BOKO: ‘IYAR NISAN DAN KA, IYAR LADAR KA’

Wannan tilastawa da aka rika yi, ta haifar da gudun hijirar da iyaye suka yi da yaran su. Wato an rika dauke yara ana tafiya da su makarantun allo a garuruwa masu nisan gaske, da nufin tserewa daga kararun ‘Nasaranci’. Wato karatun boko.

A wancan lokacin an rika kyamatar karatun zamani matuka, har aka rika yi wa iyayen yara ‘fatawar-molon-ka’ cewa iyar nisan inda ka gudu da yaron ka, to iyar yawan ladar ka a wajen Allah.

Dalili kenan sai a dauki yaro daga Funtuwa ko Kankara a kai shi karatun allo Maiduguri ko Fataskum ko Gashuwa. Wasu kuma a lula Sakkwato da su ko Kano Kaura Namoda ko Zariya.

An rika yin gugumarar yin zugar kai yara karatun allo zuwa Maiduguri, har ta kai aka rika kiran Barno da sunan “Gabas”, kamar yadda ake kiran Makka da suna “Gabas.” Shi ya a lokacin idan wani ya tafi Makka, sai a ce ya tafi “Gabas, gaba da Gabas. Wato ya tafi gaba da Barno kenan.

Yawancin yaran da ake kai wa, ba su dawowa gida sai sun sauke Akur’ani. Wani a ranar da aka yi masa sauka za a yi masa aure, wani kuma sai shekara ta kewayo.

Da haka gidajen sarakai da na jikin su su ka rika yin zurfi a cikin karatun zamani, har suka rika fita Ingila, a daya gefen kuwa yaran jama’ar karkara na kara nausawa “Gabas” su na zuwa karatun allo.

A haka aka rika tafiya tsawon lokaci, Kudu na yi wa Arewa rata wajen karatu, su kuma gidajen sarautun gargajiya da makusantan su na yi wa sauran talakawan su tazara a karatun zamani.

ILMIN ZAMANI: AN DADE DA BARIN HAUSAWA BAYA –Ibramim Kurawa

A cikin wata hira ta musammnan da PREMIUM TIMES HAUSA ta yi da Dakta Ibrahim Kurawa, wani masanin tarihi a Kano, a cikin Agusta, 2017, ya bayyana yadda tun farko aka bar Arewa, a baya a fagen ilmin zamani. Ga abin da ya ke cewa:

“Batun ilmi da ka fara yi, idan ka kalli lamarin, za ka ga cewa shi dama Bahaushe tun cikin karni na 19 har zuwa lokacin da Turawan mulki su ka shigo, bai damu da neman ilmi ba. Kai dai bar shi ga noma da fatauci kawai. Yayin da su kuma Fulani su ne malamai, su kuma ke karatun sauran fannonin ilmin musulunci.

“Wannan sai ya bai wa Fulani damar karkata zuwa ga ilmin zamani lokacin da Turawa suka shigo. Dama kuma shi kan sa ilmin zamanin a kasar Hausa dai ai ta hannun sarakunan gargajiya ya shigo, wadanda Fulanin ne, su ke mulki.

“Turawan Mulki sun rika tilasta wa sarakuna da sauran masu mulkin gargajiya su sa ‘ya’yan su makarantar boko. Dalibin farko a makarantar Gidan Danhausa a Kano, Bafulatani ne, sauran ma duk Fulanin ne duk ‘ya’yan masu mulki. Kai ko a firamare ma duk ‘ya’yan sarakuna da masu mulki ne su ka fara shiga, ko aka fara dauka.

“To haka abin ya rika tafiya. Ka ga ashe duk wanda ya kammala karatu, shi ma a gaba zai sa na sa yaran. Wadanda ba su fara karatu ba a lokacin, to za a dauki lokaci mai tsawo kafin su cimma tazarar da aka yi musu.

“Bahaushen farko da ya fara karatu a Makarantar Middle ta Kano shi ne Musa Iliyasu, ina zato a cikin 1939 ko 1940 aka sa shi makarantar. Malam Aminu Kano ma ya riga shi shiga kenan, domin shi tun a wajajen 1936 ya shiga Makarantar Katsina. To sai ka duba da kyau, Bello Kano, Dokaji, Ahmadu Matidan, Sani Dan Ciroma duk sun riga Musa Iliyasu shiga da shekaru kusan 20. Domin su tun a 1921 or 1922 su ka shiga. Dukkan su kuma Fualani ne idan ka debe Matidan, wanda shi Balaraben Kano ne.

“Dalibin farko a Kwalejin Barewa ina jin a cikin 1923, mai suna Abubakar, Bafulatani ne daga Sokoto. Shi aka fara dauka a tarihin Kwalejin Barewa. Shi ne ma ya zama Madakin Sokoto daga baya. Dalibi na hudun dauka, Ahmadu Matidan ma dan Kano ne, amma Balarabe. Ahmadu Bello shi ne wanda ya fara zuwa Kwalejin Katsina daga cikin jinin Shehu Danfodiyo. Ina jin wajajen 1926. Da wannan ilmin ne Fulani su ka fara shiga gaban Hausawa wajen aikin gwamnati da kuma mulki na siyasa a tarihin Nijeriya.”

Inji Kurawa, wanda ya yi Daraktan Bincike da Tattara Bayanai a zamanin Gwamnatin Ibrahim Shekarau, a Jihar Kano.

Bayan kafa jami’o’i a Arewa, ilmin zamani ya samu tagomashin karbuwa ganin yadda aka karbi mulki a hannun Turawa, kuma dukkan al’amurran tafiyar da mulki, gudanarwarwa da gwamnati duk sun koma karkashin ’yan kasa.

Amma duk da haka, kudu ta yi wa Arewa fintinkau ko a lokacin, domin ta kasance yawanci ’yan kudu ne suka yi kaka-gida a kan mukamai da yawa a Arewa.

AREWA: GA JAMA’A AMMA BABU JAMI’A

A yau ba jiya ba kuma ba gobe ba, idan aka auna yawan jami’o’in da ba na gwamnati ba, wadanda aka kafa a kudancin kasar nan, za a ga cewa an yi wa Arewa fintinkau a fannin neman ilmin zamani.

Ba don an yi sa’a gwamnonin jam’iyyar PDP sun gina jami’o’i na Gwamnatin Jiha a jihohin su ba, to da tabarbarewar ilmin jami’a a Arewa ya yi muni sosai yanzu a Arewa.

Gwamnonin PDP sun kafa jami’ar Jiha a Katsina, Gombe, Jigawa, Kano, Kaduna da sauran Jihohi da dama a Arewa. Wannan ya kara yawan jami’o’i a Arewa, amma kuma babu yawan masu zaman kan su kamar kudancin kasar nan

KUDU NA JAMI’A AREWA NA JAMA’A

Kididdiga ta tabbatar da cewa a yanzu haka akwai jami’o’I masu zaman kan su wadanda ban a gwamnati ba a Yankin Kudu maso Yamma har guda 36. Jihohin Kudu maso Yamma su ne Lagos, Ogun, Ondo, Oshun, Ekiti.

A jihohin Kudu maso Kudu kuwa akwai jami’o’i wadanda ba na gwamnati ba har 14. Jihohin Kudu maso Kudu sun hada da Bayelsa, Rivers, Cross River, Akwa Ibom.

Yankin Kudu maso Gabas da ya kunshi Enugu, Anambra, Abia, Imo da Ebonyi, akwai jami’o’i da ba na gwamnati ba har 13.

Amma kakaf a fadin Yankin Arewa maso Yamma, wato jihohin Kano, Kaduna, Katsina, Zamfara, Sokoto, Kebbi da Jigawa, jami’a guda 3 ce rak ta masu zaman kan su.

Wannan yanki na Arewa maso Yamma shi ne ya fi yawan jama’a a Najeriya, yawan jama’a a Arewa, kuma shi ne ya fi samar da yawan kuri’u a zabe.

Arewa maso Gabas da ya hada da Gombe, Adamawa, Bauchi, Yobe da Barno, akwai jami’a 2 kacal.

Wannan yanki ne Boko Haram ya yi katuru, wanda ya samo tushen fitinar sa daga haramta karatun boko.

Yankin Arewa ta Tsakiya, da ya hada da FCT Abuja, Neja, Plateau, Benuwai, Nasarawa, Kwara, Kogi da Taraba, akwai jami’o’i masu zaman kan su guda 11.

Idan aka hada jimmila za a ga cewa a Arewa gaba daya akwai jami’o’i 16, su kuma Kudu akwai 63, duk masu zaman kan su, wadanda bana gwamnatin jiha ko na tarayya ba.

RASHIN JAMI’O’I A AREWA: Wani Babban Cikas

Baya ga tazarar da aka yi wa Arewa a jami’o’j masu zaman kan su, to wata babbar tazara kuma ita ce a addinance ma an yi wa musulmai tazara wajen kafa jami’o’i.

Wadannan jami’o’i na Kiristoci, ba fa addinin kiristancin zunzurutu suka koyarwa ba, sun a koyar da fannoninn ilmin zamani ne ne, kamar yadda sauran jami’o’in Gwamnatin Tarayya, na Jihohi da sauran na masu zaman kan su ke koyarwa.

Bincike ya nuna cewa akwai jami’o’i 32 mallakar manya-manyan coci-coci na kasar nan. Amma jami’o’i 2 ne rak mallakar kungiyoyin musulunci a nan kasar.

Sannan kuma baya ga jami’o’i 32 da coci-coci na Kiristoci suka mallaka, akwai ma wasu guda 15 a yanzu haka da wasu manyan coci-coci na kasar nan ke jira a ba su lasisi su kafa.

Karin tazara da aka yi wa Arewa wajen jami’a kuma ita ce jami’ar nan ta Gwamnatin Tarayya, wadda ake yin karatu daga gida, wato National Open University of Nigeria (NOUN).

Cikin watan Maris, 2019 ta yaye dalibai 20,799, amma kusan kashi 80 bisa 100 duk ‘yan kudu ne.

Sannan kuma ta na da dalibai sama da 400,000, amma kusan kashi 80 duk ‘yan kudu ne daliban. ’Yan Arewa ba su cika maida hankali wajen shiga jami’ar ba, sai cikin shekarun nan uku, bayan an bai wa Farfesa Abdalla Uba Adamu na Jami’ar Bayero ta Kano shugabancin jami’ar sannan aka karkato da hankulan ‘yan Arewa shiga jami’ar ta NOUN.

A karshe, cikin makon da ya gabata an bayyana cewa akwai jami’o’I 303 da ake son a yi wa rajista a kasar nan?

Shin nawa ne a cikin su za a kafa a Arewa? Kada fa mu Arewa ta shankake har sai Chana ta zo ta yi mana kaka-gida a fannin ilmi a Arewa, kamar yadda yadda suka yi kaka-gida a harkokin kasuwanci a Kano.

Tags: ABUAbujaBokoBUKHausajami'oiKaratuLabaraiNajeriyaNewsPREMIUM TIMESSokotoUDUZaria
Previous Post

HOTUNA: Yadda mazauna Unguwannin Kaduna suka yi zanga-zangar kira ga gwamnati da ta kawo karshen ayyukan mahara

Next Post

ILMIN ZAMANI: An dade da barin Hausawa a baya –Ibramim Kurawa

Next Post
pupils_of_dukawiya_science_p.s_in_computer_class_gwale_lgea

ILMIN ZAMANI: An dade da barin Hausawa a baya –Ibramim Kurawa

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Boko Haram sun kashe mutum 32 a Barno
  • YUNƘURIN KASHE ABBA KYARI A KURKUKU: Ana shirin maida shi a hannun SSS
  • FIDDA GWANIN APC A KADUNA: Yadda surikin Buhari ya ƙi yarda El-Rufai ya yi masa yankan-gishirin-Malam, gagagir, gagagir
  • ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP
  • SHIRIN CIYAR DA ƊALIBAI: Gwamnati za ta kashe naira miliyan 999 a kullum wajen ciyar da ‘yan makaranta miliyan 10

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.