Makonni biyu kafin zaɓen fidda-gwanin ‘yan takara a Najeriya, bishiyoyin jam’iyyar PDP da APC sun yi yaushi a Kano, sakamakon gatarin da jam’iyyar NNPP ta yi amfani da shi ta sare rassan PDP, sannan ta tsallaka cikin gonar APC ta jijjige bishiyar.
Kusan za a ce APC da PDP a Kano dai sun yi yaushin da ko an shekara ana zuba masu ruwa, bishiyoyin biyu ba za su sake tohon sabon ganye ba.
Jam’iyyar NNPP wadda ba a sani ba kafin jagoran Kwankwasiyya Rabi’u Kwankwaso ya shiga jam’iyyar, a yanzu ta zama abin tsoro a Kano, jihar da ta fi sauran jihohin Najeriya yawan masu jefa ƙuri’a. Kuma jihar da kowane ɗan takarar shugaban ƙasa ke tsananin so ya lashe a lokacin zaɓe.
Shi kan sa uban jam’iyyar NNPP ya yi mamakin ganin yadda jam’iyyar ta yi saurin samun tagomashi a Arewacin Najeriya. Dalili kenan ya rasa ta cewa, sai ya ce “wannan kuma wata mu’ujiza ce daga Ubangiji kawai.” Haka Boniface Aneboanam ya furta.
Ba wani abu ya yi saurin ƙara wa NNPP ƙarfi a Kano ba, sai gagarimin rikicin da ya tirniƙe PDP mai adawa da kuma APC Mai mulki a jihar.
Kwankwaso ya fice daga APC bayan da aka sake naɗa Abdullahi Abbas shugabancin jam’iyyar APC.
Sannan kuma rikicin cikin gidan PDP da su Wali ya sa Kwankwaso ficewa daga PDP.
A wani ɓangare can kuma APC na fama da na ta rikice-rikicen a Kano, biyo bayan ƙaƙaba Mataimakin Gwamna Nasiru Gawuna da Gwamna Ganduje ya yi, a matsayin wanda zai yi takarar gwamna a APCin Kano a zaɓen 2023.
Dama tun a wurin zaɓen shugabannin jam’iyya an samu mummunar ɓaraka a tsakanin ɓangaren Abdullahi Abbas wanda Gwamna Ganduje ke mara wa baya da kuma ɓangaren Haruna Ɗanzago, wanda Sanata Shekarau da Sanata Barau Jibrin ke mara wa baya.
Bayan zaɓe an ci gaba da shari’a har zuwa Kotun Ƙoli, inda aka bai wa ɓangaren Abdullahi Abbas rinjaye.
Wannan ya kawo ɓarkewar APC inda manyan ‘yan jam’iyyar su ka yi ta tururuwa cikin NNPP.
Guguwar ‘Fecewar’ ‘Yan APC Zuwa NNPP A Kano:
Jiga-jigan APC, ‘Yan Majalisar Tarayya da Shugaban Ma’aikatan Gidan Gwamnati sun saki Ganduje sun kama Kwankwaso a NNPP.
Yayin da guguwar sauyin sheƙa ta murtuke jam’iyyar APC a Kano, har ta hana Gwamna Abdullahi Ganduje barci mai nauyi, yanzu kuma wasu manya kuma jiga-jigan gwamnati da jam’iyya sun ƙara ficewa daga APC a Kano, su na komawa NNPP, jam’iyyar Kwankwaso.
‘Yan Majalisar Tarayya biyu, Tijjani Joɓe da Badamasi Ayuba, tare da Shugaban Ma’aikatan Gidan Gwamnatin Jihar Kano, Ali Makoɗa sun fice daga APC, sun koma NNPP.
Ficewar ta su dai ya tabbatar da cewa manyan ‘yan APC za su tsiyaye daga jam’iyyar su sauya sheƙa, biyo bayan yadda Gwamna Abdullahi Ganduje ya tsayar da Mataimakin Gwamna Nasiru Gawuna a matsayin ɗan takarar APC, yayin da Kwamishinan Ƙananan Hukumomi, kuma zai yi masa mataimaki a takarar zaɓen 2023.
Sauran waɗanda su ka fice ɗin sun haɗa da Ahmed Muhammadu, Mai Binciken Kuɗi na APC na Jihar Kano; Umar Maitsidau, Shugaban Matasan APC na Kano, kuma tsohon Shugaban Ƙaramar Hukumar Makodai da kuma wasu fitattu a siyasar Kano.
Dama kuma tsohon Kakakin Majalisar Kano, wanda a yanzu Ɗan Majalisar Tarayya ne, Alhassan Rurum da Kawu Sumaila da Aminu Garo, duk sun fice daga APC.
Shugaban Ma’aikatan Gidan Gwamnati Ali Makoɗa dama ya aika wa Gwamna takardar ajiye aiki domin ya tsaya takara, amma sai Ganduje ya shawarci shi ya ci gaba da aikin sa, ya ƙi karɓar takardar ajiye aikin da ya aika masa.
Amma a ranar Juma’a ya tabbatar da ajiye aikin sa, kuma ya shaida cewa ya koma NNPP.
Ɗan Majalisar Tarayya Tijjani Joɓe ya shaida wa PREMIUM TIMES cewa ya fice daga APC zuwa NNPP, domin ci gaba da samar wa al’ummar Mazaɓar sa ayyukan inganta rayuwa.
Alamomin Watsewar Ɗaurin Tsintsiya A Kano:
A wani labarin alamomin watsewar ɗaurin tsintsiyar APC a Kano, PREMIUM TIMES Hausa ta buga labarin cewa Mataimakin Kakakin Majalisa ya fice daga APC, ya koma PDP.
Mataimakin Kakakin Majalisar Jihar Kano, Zubairu Hamza Masu ya fice daga APC, ya koma PDP.
Ya yi wannan sanarwa ce a ranar Alhamis, inda ya ce ya koma jam’iyyar adawa PDP, a cikin wata wasiƙa da ya aika wa Shugaban APC na Mazaɓar Masu, cikin Ƙaramar Hukumar Sumaila.
Ya rabbata dalilai na rikice-rikicen da su ka dabaibaye APC da kuma hususan tsagwaron rashin adalcin da ya ce ana shukawa a cikin APC.
Masu ya ce a cikin APC an maida Shiyyar Kano ta Kudu saniyar-ware, ba a bayar da dammamakin da ya kamata a riƙa bai wa yankin kamar yadda dimokraɗiyya ta shimfiɗa.
Daga baya Masu ya shaida wa manema labarai cewa akwai misalin wani rashin adalcin da aka yi wa tsohon Babban Hadimin Shugaban Ƙasa Kawu Sumaila, wanda Masu ya ce shugabanin jam’iyyar APC ne su ka yi masa na Jihar Kano.
“Idan ku ka duba, za ku ga cewa ba a yi wa Kawu Sumaila adalci a zaɓen 2019 ba. Amma mu ka haƙura a lokacin, saboda jam’iyya ta taushi ƙirjin mu.
“To yanzu kuma tuni har mun fara ganin alamomin za a sake maimaita mana rashin adalcin da aka yi mana a 2019. Saboda haka mu ka ga gara tun a yanzu kawai mu yanke matsayar da za mu ɗauka domin gyara wa kan mu rashin adalcin da aka yi mana a baya.” Inji Zubairu Masu.
Idan ba a manta ba, Kawu Sumaila ya tsaya takarar fidda-gwani na ɗan takarar Sanatan Kano ta Kudu a zaɓen 2019. Amma Kabiru Gaya ya kayar da shi, a zaɓen da ɗimbin ‘yan cikin APC da wajen ta su ka yi iƙirarin cewa an zabga wa Sumaila maguɗi. Wasu ma na cewa fashi aka yi masa da rana kata.
Sumaila ya ƙalubalanci sakamakon zaɓen, amma uwar jam’iyya a Kano ta ba shi haƙuri, ta ce ya karɓi ƙaddara, ta riga fata.
Akwai alamomi masu ƙarfin da ke nuni da cewa Sumaila zai fice daga APC ya koma NNPP, jam’iyyar su Rabi’u Kwankwaso a Kano.
Alamomin Watsewar Ɗaurin Tsintsiya A Kano:
Mataimakin Kakakin Majalisa ya fice daga APC, ya koma PDP.
Mataimakin Kakakin Majalisar Jihar Kano, Zubairu Hamza Masu ya fice daga APC, ya koma PDP.
Ya yi wannan sanarwa ce a ranar Alhamis, inda ya ce ya koma jam’iyyar adawa PDP, a cikin wata wasiƙa da ya aika wa Shugaban APC na Mazaɓar Masu, cikin Ƙaramar Hukumar Sumaila.
Ya rabbata dalilai na rikice-rikicen da su ka dabaibaye APC da kuma hususan tsagwaron rashin adalcin da ya ce ana shukawa a cikin APC.
Masu ya ce a cikin APC an maida Shiyyar Kano ta Kudu saniyar-ware, ba a bayar da dammamakin da ya kamata a riƙa bai wa yankin kamar yadda dimokraɗiyya ta shimfiɗa.
Daga baya Masu ya shaida wa manema labarai cewa akwai misalin wani rashin adalcin da aka yi wa tsohon Babban Hadimin Shugaban Ƙasa Kawu Sumaila, wanda Masu ya ce shugabanin jam’iyyar APC ne su ka yi masa na Jihar Kano.
“Idan ku ka duba, za ku ga cewa ba a yi wa Kawu Sumaila adalci a zaɓen 2019 ba. Amma mu ka haƙura a lokacin, saboda jam’iyya ta taushi ƙirjin mu.
“To yanzu kuma tuni har mun fara ganin alamomin za a sake maimaita mana rashin adalcin da aka yi mana a 2019. Saboda haka mu ka ga gara tun a yanzu kawai mu yanke matsayar da za mu ɗauka domin gyara wa kan mu rashin adalcin da aka yi mana a baya.” Inji Zubairu Masu.
Idan ba a manta ba, Kawu Sumaila ya tsaya takarar fidda-gwani na ɗan takarar Sanatan Kano ta Kudu a zaɓen 2019. Amma Kabiru Gaya ya kayar da shi, a zaɓen da ɗimbin ‘yan cikin APC da wajen ta su ka yi iƙirarin cewa an zabga wa Sumaila maguɗi. Wasu ma na cewa fashi aka yi masa da rana kata.
Sumaila ya ƙalubalanci sakamakon zaɓen, amma uwar jam’iyya a Kano ta ba shi haƙuri, ta ce ya karɓi ƙaddara, ta riga fata.
Akwai alamomi masu ƙarfin da ke nuni da cewa Sumaila zai fice daga APC ya koma NNPP, jam’iyyar su Rabi’u Kwankwaso a Kano.
Ƙarshen Alewa Ƙasa: Dalilin Ficewa Ta daga APC -Abdulmumin Jibrin:
Tsohon Shugaban Kwamitin Kasafin Kuɗi a Majalisar Tarayya, Abdulmumin Jibrin, ya fitar da sanarwar dalilan ficewar sa daga APC zuwa NNPP.
Jibrin, wanda na hannun daman ɗan takarar shugaban kasa ne, Bola Tinubu, ya ragargaji wani babba a ƙasar nan da ya ce shi ne dalilin ficewar sa, saboda ya na ƙoƙarin ganin ya kashe masa tasirin siyasa, tun lokacin dusashewar hasken ta bai yi ba.
Duk da Jibrin Kofa bai ambaci sunan babban da ya ke nufi ba, amma dai makusantan sa na cewa da Gwamna Ganduje na Kano ya ke.
Amma dai har yanzu PREMIUM TIMES ba ta kai ga tabbatar da hakan ba.
“Na Fice Daga APC Saboda Wani Babban Ɗan Gudubale Na Ƙoƙarin Kashe Hasken Siyasa Ta -Abdulmumin Jibrin:
“Tsawon shekaru 9 kenan ina sadaukar da dukiya ta da ilmi na da siyasa ta wajen ganin na taimaka wajen ciyar da APC a gaba.
“A matsayi na na Shugaban Kwamitin Kasafin Kuɗaɗe na Majalisar Tarayya, a cikin 2013, na yi kasadar jagorancin wakilan tarayya 60 daga PDP zuwa APC. Ni na samar da kuɗaɗen ɗaukar nauyin wurin da mu ka yi taron da haifar da gurguntawar da mu ka yi wa PDP mai mulki a lokacin.
“A lokacin na sha fama da ƙiyayya da barazana, bi-ta-da-ƙulli kala-kala daga gwamnatin PDP mai ci a wancan lokacin.
“A 2015 kuma na zama Shugaban Kwamitin Kasafin Kuɗaɗe na Majalisar Tarayya, an yi ƙulle-ƙullen da ya haifar da dakatar da ni a majalisa, tsawon shekaru biyu. A lokacin da na koma Majalisa, na samu shugabannin ta na faman rigima da gwamnati. A lokacin APC da gwamnati a lokacin.
“Ganin haka na tashi tsaye haiƙan mun kafa Ƙungiyar Kare Muradun Buhari a Majalisar Tarayya. A Majalisar Dattawa kuwa Sanata Abdullahi Adamu ne ya jagoranci wannan ƙungiya.”
Jibrin ya ce a lokacin da ya ci zaɓe a 2019, ya yi ƙoƙarin zama Kakakin Majalisar Tarayya, amma uwar jam’iyya ta taushi zuciyar sa, ta ce ya haƙura, za a yi karɓa-karɓa ne.
Ya ce haka ya haƙura, ya ci gaba da yi wa Kakakin Majalisar Tarayya na yanzu kamfen.
“Haka mu ka sadaukar da komai na mu ga jam’iyyar da ko na gode da Allah-sam-barka’ ba tayi mana ba, sai ma jefa mu a cikin kwandon shara da ta yi.”
Shugabancin Hukumar Gidaje Ta FHA Da Aka Ba Ni, Ba Wani Kayan Gabas Ba Ne -Abdulmumin Jibrin:
Jibrin ya ce kowa ya tabbatar da cewa shi ne ya yi nasara a zaɓen 2019 na Majalisar Tarayya. Amma aka haɗa baki da wasu ƙusoshin jam’iyya aka yi masa yankan baya. A kotu kuma aka yi masa ‘shari’a-saɓanin-hankali.
“Bayan an ba ni shugabancin Hukumar Gidaje ta FHA, sai na gane ai hukumar ba wani kayan gabas ba ce, wurin cike ya yake da kitimirmira. Har ma gara majalisa da Hukumar FHA, muƙamin da dama na karɓa ne kawai don kishin ƙasa ta.”
Tsakani Na Da Ɗan Gudubalen Da Ke Neman Ganin Baya Na – Abdulmumin Jibrin:
Abu mafi firgitarwa da tayar da hankali da na fuskanta a cikin shekaru bakwai ɗin nan, shi ne yadda wani babban ɗan gudubale ke ta ƙoƙarin ya lalata ko ya tarwatsa duk wani wanda ya ke ganin wata barazana ce a wurin sa.
“Munin halayen wannan ɗan gubale ya kama da yadda Turawan Afrika ta Kudu su ka riƙan nuna wa baƙaƙen fatar ƙasar ƙiyayyar wariyar launin fata.
“A ƙarshe dai na zauna na yi karatun-ta-natsu, na ga har gara kawai na tashi na kare mutunci na daga bin wani ɗan gudubalen da a kullum shi so ya ke ya ga mabiyan sa na bauta masa. To ni ba zan zama bawa haka kawai don na yi wa wani biyayya ba. Ehe!”
Jibrin ya ci gaba da bayyana abin da ya kira tantagaryar rashin mutuncin da wannan babban ɗan gudubale ke gantsara masu a APC.
Ya ce kwanan nan sun yi doguwar magana ta waya, “har dai da na ga rashin mutuncin na sa ya kai ƙololuwa, na yi ta-maza na ce da shi, ‘yanzu kai a matsayin ka na uban mu a tafiyar siyasa, za ka yi farin ciki nan gaba idan ka ga mu na gantsara wa ‘ya’yan cikin ka irin rashin mutuncin da kai ka ke yi mana?”
Na Fice Daga APC, Na Ajiye Farantin Tallar Tinubu, Na Kama Kwankwaso:
Jibrin ya nuna matuƙar godiya ga Shugaba Muhammadu Buhari, wanda ya ce zai riƙe shi a matsayin uba, har a bayan zaɓen 2023.
Sannan kuma ya yi sanarwar ficewa daga APC zuwa jam’iyyar NNPP, mai kayan marmari.
A ƙarshe ya ce ya ajiye tallar Bola Tinubu, tallar da ya ce ko da shi ko babu shi, Tinubu na da ‘yan talla masu yawan da ficewar Jibrin daga rukunin masu kamfen ɗin Tinubu ba zai rage kamfen ɗin da komai ba.
Tasirin NNPP Wajen Zaizayewar Fentin APC A Kano:
Yayin da zaɓen fidda-gwani ke ƙara gabatowa, manyan jam’iyyu biyu na APC da PDP na fuskantar gagarimar matsala.
A gefe ɗaya PDP ta yi tsaye cak a cikin tasha babu fasinja, ita kuwa motar APC da rigaya ta cika maƙil da lodi, manyan fasinjojin cikin ta sai sauka su ke yi sanadiyyar rikicin da ya ɓarke tsakanin mai mota, direba, ‘yan kamasho da ‘yan ka-yi-na-yi, waɗanda su ka yi mata lodi.
Bisa dukkan alamu NNPP za ta kawo wa jam’iyyun biyu babbar matsala a zaɓen 2023, ganin yadda masu fita daga motar APC da ta PDP na sungumar kayan su su na shiga motar NNPP.
Babu ɗan takarar shugaban ƙasa da zai yi murna da rashin nasarar sa a Kano, jihar da ta fi kowace jiha samun yawan masu jefa ƙuri’a.
Tasirin NNPP: Yadda Kwankwaso Ke Karakainar Zawarcin Shekarau:
A cikin ƙasa da sa’o’i 30, Kwankwaso ya kai ziyara gidan Shekarau a cikin Kano, ziyarar da ake ganin alamomi ne na haɗewar manyan ‘yan siyasar biyu.
Ƙwaƙƙwarar majiya ta shaida wa PREMIUM TIMES HAUSA cewa a yau Laraba ce Shekarau zai yi wa ɗimbin magoya bayan sa na Shiyyar Sanatan sa na Kano ta Tsakiya jawabin ficewa daga APC zuwa NNPP.
Shekarau ya samu matsala a APC, ganin yadda Sanata Basheer Lado ya fito takarar kujerar sa ta Sanata.
Ana ji-ta-ji-tar cewa Ganduje ya ɗaure wa Lado gindi, amma dai Lado ɗin ya ƙaryata hakan.
Idan Shekarau ya koma NNPP, mai yiwuwa ya samu kujerar sa, inda zai gabza takara da Lado a babban zaɓe.
Wannan babban zaɓe dai ko tantama babu ba zai yi wa APC da PDP daɗi a Kano ba. Saboda NNPP ta kawo ƙarfi.
Hausawa kuma na cewa, “Na kawo ƙarfi, ya fi wane ya girme ni.”