Rundunar Sojin Najeriya ta sanar da cewa daga yau kungiyar masu fafutikar kafa kasar Biafra IPOB sun zama kungiyar yan ta’adda a kasa Najeriya.
Rundunar Sojin ta sanar da haka ne yau a wata sanarwa da ta fitar yau.
Tace bayan ta kammala duba dukkan bayanai akan ayyukan kungiyar ta gamsu cewa kungiyar ‘yan Ta’adda ne a kasar nan.
Cikin dalilan da Rundunar Sojin ta bayar da sune suka zama hujjojinta na yin haka hada da:
1 – Kungiyar ta kafa wata rundunar mayaka na sirri
2 – Ta kafa jami’an tsaro na Biafra mai suna ‘Biafra National Guide’
3 – Suna yi wa mutane kwace a hanyoyi
4 – Kai farmaki da makamai ga jami’an yan’sanda da Sojoji
5 – Sun kai wa Sojoji hari cikin jagorancin shugabansu Nnamdi Kanu da kokarin kwace makamin wani soja.
6 – Neman kwace bindigar wata jami’ar soja.
” Rundunar Soji ta na kira ga iyaye da su gargadi ya’yansu su nisanci shiga kungiyar IPOB din domin duk wanda aka samu aciki ya zama dan ta’adda.”
Discussion about this post