• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Zamfarawa Dukiyar Ku Ce Da Aka Sace, Don Haka Ku Shiga Taitayin Ku! Daga Imam Murtadha Gusau

Mohammed LerebyMohammed Lere
May 8, 2021
in Ra'ayi
0
Dole A Dakatar da Kashe Ƴan Arewa a Kudu -Gwamna Matawalle

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinkai

Assalamu Alaikum

‘Yan uwa na Zamfarawa! Wallahi ni har kullun ni kan yi mamaki kuma ni kan ji haushi da bakin ciki akan wasu lamurra da har yau akwai alamun cewa, ‘yan uwana talakawan jihar Zamfara sun kasa ganewa, kuma sun kasa fahimta. Misali, mutun ne zai shiga siyasa, shi ba kowa ba, kuma shi ba dan kowa ba. Shi ba dan kasuwa ba, kuma shi ba wani kasurgumin ma’aikacin gwamnati ba ko wani hamshakin dan kwangila ba. Ko da ya shiga siyasa, kowa yasan cewa baya da komai, wallahi ba shi da ko sisi, kawai yawo yake yi yana maula da banbadanci da roko a gidajen ‘yan siyasa. An san shi, an san iyayensa, an san asalinsa, an san tarihinsa, an san dukkanin zuri’arsu. Kowa ya shaida cewa shi dan talakawa ne iri na, amma kawai daga ya samu dama, bisa kaddarar Allah, da kuma sanadiyyar wasu mutane da suka daga shi sama, suka taimakeshi, suka tallafa masa, ya shiga siyasa, har Allah cikin ikon sa ya kaddari ya zama gwamnan jiha, yayi shekaru takwas yana matsayin gwamnan jiha, bayan wasu kananan mukaman siyasa da ya taba rike wa, sanadiyyar dai wadancan manyan mutane, bayin Allah, mutanen kwarai, wadanda basu da hassada da ganin kyashi; wadanda Allah yayi amfani da su suka tallafa masa, suka daga shi sama har ya zama wani abu a jihar. Kawai daga wannan, shi yanzu yana ganin ya zama biloniya, ya tara kudi, ta hanyar sace dukiyar jiha, ta hanyar kassara jihar, wanda har yake ganin yanzu, shi karfin shi ya kawo, wai shi zai iya ja da ikon Allah, wai zai iya ja da zabin Allah, zai iya ja da hukuma ko gwamnatin jiha!

Ya ku ‘yan uwa na talakawan jihar Zamfara, ku sani, wallahi a gaban idon mu aka kirkiro jihar Zamfara, duk gwamnonin da aka yi a jihar Zamfara a gaban idon mu suka yi mulki suka gama, suka wuce. Tun daga Jibril Bala Yakubu, har zuwa Yarima, har zuwa Dallatu, wallahi bamu gani ba, kuma bamu ji cewa sun saci kudin al’ummah ba, bamu ga sun sace dukiyar jiha ba, basu sace dukiyar talakawa ba, basu jefa al’ummah cikin wahala, da kangi da kunci ba, bare wai har suce zasu yi amfani da dukiyar da suka sata ta jiha, su rinka sayen tirelolin abinci da milliyoyin dabbobi suna rabawa magoya bayansu na siyasa. Kawai abun da muka shaida game da su shine, wadancan tsoffin gwamnoni da suka shude, suna taimakawa talakawa ne da magoya bayan su, gwargwadon iyawarsu, da dan abunda Allah ya hore masu, kasancewar duk mun shaida cewa basu yi sata ba, kuma basu zalunci talakawan su da al’ummarsu ba!

Amma da yake mu talakawan jihar Zamfara, har yanzu, wasu daga cikin mu sun kasa ganewa, mun kasa fahimta, wasun mu basu waye ba, daga kawai mutum yayi gwamna, ya sace maku dukiya, yazo kuma yana sawo kayan masarufi yana rabawa magoya bayan sa, shike nan sai muyi ta ganin cewa wai taimako yake yi, wai abun kirki yake yi.

Shin kun manta da cewa, watakila da bai sace wannan dukiyar taku ba, da an samu tsaro da taimakon Allah, da an samu ruwan sha masu tsafta, da an samu ingantaccen ilimi, da an samu ingantacciyar wutar lantarki, da an samu magani kyauta a asibitocin mu, da an samu ingantattun hanyoyi da sauran kayayyakin more rayuwa a jihar Zamfara!

Kawai mutum ya halaka ku, ya sace maku dukiya, ya kashe ku, amma don ya dan tsakuri wani abu daga cikin dukiyar ku da ya debe, yana rabawa magoya bayansa dan wani abu, yana bushasha iya son ran sa, wanda kowa yasan wallahi ba don Allah yake yi ba, kawai yana yi ne domin ya kara rikita jihar Zamfara, ya kara jawo muna matsalolin rashin tsaro, ya zuga talakawa domin su bijirewa gwamnati mai ci, ta Matawalle zabin Allah, wanda dama can muna sane da halin da jihar mu take ciki, na halin rashin tsaro, wanda nayi imani da Allah cewa, shi wancan azzalumin mutum, yana daga cikin wadanda basu so wannan matsala ta kare ta jihar Zamfara, sannan yana daga cikin wadanda suka haddasa muna wannan bala’i a jiha!

Saboda haka, wallahi ina kira da babbar murya, kuma tsakanina da Allah, cewa, talakawan jihar Zamfara muyi hankali, ya zama tilas mu shiga taitayinmu, mu goya wa gwamnatin Matawalle baya, muyi masa addu’o’i, mu rokar masa Allah ya bashi nasara, muyi masa fatan alkhairi, da rokon gamawa lafiya.

Sam, kar mu yarda wasu shedanu, mashaya jinin bayin Allah, ‘yan iska, wadanda basu nufin jihar mu da alkhairi, su zuga mu, su kai mu su baro, da sunan wai wata adawar siyasa ta shedanci. Wallahi mun fi kowa sanin halin da jihar mu take ciki, na matsalar rashin tsaro. Don haka duk wanda yazo muna da wani rikici, ko wata hayaniya, ko wani rudu, da sunan wai shi dan adawar siyasa ne, ko da sunan wa’azi, don Allah, don Allah, don Allah ina rokon ku, da mu kunyata shi, ko shi waye, kuma ko shi dan gidan waye. Domin duk tunanin da mutum yake yi, wallahi mu jihar mu tafi shi daraja da matsayi a wurin mu, domin bamu da wani wurin da yafi muna jihar Zamfara a duniya!

Wallahi in dai har da gaske muke yi, muna son ci gaban jihar Zamfara da zaman lafiyar ta; in dai har muna son a samu zaman lafiya, muna son Allah ya tausaya muna, ya kawo muna karshen matsalolin da suka dabaibaye jihar mu, to ya zama tilas mu hada karfi da karfe, mu hada hannu, mu goyi bayan gwamnatin Bello Matawalle, muyi masa addu’a da fatan alkhairi!

Wallahi, Allah ya sani, kuma shine shaida, ni ban san Bello Matawalle ba, kuma shi bai san ni ba, to amma ni ina kishin jiha ta ta Zamfara tsakanina da Allah, kuma matsalolin jihar suna damu na matuka. Domin Allah ya sani, kuma shi shaida ne akan haka, kullun, da su nike kwana, kuma da su nike tashi!

Kuma wallahi ku sani, duk abunda Sheikh Sa’idu Aliyu Maikwano ya fadi a wurin tafsirinsa game da gwamna Matawalle da gwamnatinsa gaskiya ne, kuma ya zama tilas, kuma wajibi, kuma dole dukkanin Zamfarawa su rungumi wannan bayani nasa mai albarka, kuma suyi na’am da shi yadda ya kamata. Idan ba haka ba kuwa, wallahi zamu yi dana-sani! Allah ya sawwake, amin.

Ya ku ‘yan uwa na Zamfarawa masu daraja, ku sani, wallahi ina yi maku wannan bayani ne tsakanina da Allah, kuma domin Allah. Don haka ya rage namu, idan mun ji to sai Allah ya taimake mu, amma idan mun bijire, muka yi kunnen uwar shegu da wannan bayani, to mune zamu sha wahala ba wasu ba. Ko kuma in ce mune muke shan wahala ba wasu ba! Ina rokon Allah ya sawwake, amin.

Sannan ya zama tilas muyi hattara, kuma mu kiyaye, domin mutum ko shi malamin addini ne, in dai har muka ga alamun cewa zai kawo muna rudani da hayaniya a jihar mu, to ya zama dole mu ce masa ba mu yarda ba, kuma mu kauracewa shedancinsa da wawancinsa. Domin ba zai yiwu ba, mutum da sunan malanta, ko da sunan wai wata adawar siyasa, ya kara jefa mu cikin rudani da hayaniya marasa amfani! Mu jihar mu wallahi tafi karfin wani maganar APC ko PDP a wurin mu. Mu zaman lafiya muke bukata a halin yanzu ba wani abu ba. Don haka ya zama tilas mu goyi bayan gwamnatin Matawalle, a kokarin ta, tare da taimakon Allah da iyawarsa, na neman mafita da samar da zaman lafiya jihar.

Ya ku ‘yan uwana Zamfarawa, wallahi a halin yanzu kasar mu Najeriya da jihar mu ta Zamfara, da sauran jihohi, addu’a suke bukata, ba wata hayaniya ta shirme ba, ko wata adawar siyasa marar amfani ga talakawa ba.

Ina addu’a da rokon Allah yasa mu gane, amin.

Wassalamu Alaikum

Nagode

Dan uwanku, Imam Murtadha Muhammad Gusau ne ya rubuto daga Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samun sa a lambar waya kamar haka: 08038289761.

Tags: AbujaHausaLabaraiMatawalleNajeriyaNewsPREMIUM TIMESZamfara
Previous Post

An damke wanda ya yi ‘kashin’ kullin hodar Ibilis 59 a filin jirgin saman Abuja

Next Post

El-Rufai na daga cikin wadanda suka kai Buhari suka Baro – In ji Gwamnan Benuwai, Ortom

Mohammed Lere

Mohammed Lere

Next Post
El-Rufai na daga cikin wadanda suka kai Buhari suka Baro – In ji Gwamnan Benuwai, Ortom

El-Rufai na daga cikin wadanda suka kai Buhari suka Baro - In ji Gwamnan Benuwai, Ortom

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN KASA: Atiku ya kai wa kotu tulin hujjoji daga na’urar BVAS a zaɓen 2023
  • Dikko Radda zai saka tsarin TSA a duka harkokin shige da ficen kudaden jihar Katsina
  • Dalilin da ya sa na canja sunan titin Raba zuwa titin ‘Nasir El-Rufai – Gwamna Uba Sani
  • KOKAWAR ƘWACE KUJERAR TINUBU: Kotu ta karɓi kwafen takardun zargin Asiwaju ya yi harƙallar muggan ƙwayoyi
  • SIYASAR KANO: Gwamna Abba ya soke naɗe-naɗe, ya ƙwace filaye da kadarorin da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.