A ranar Laraba ne jami’in hulda da jama’a na hukumar kula da alhazai na jihar Zamfara Yakub-Yahaya Talatan-Mafara ya sanar cewa an fara jigilar alhazan jihar daga kasar Saudiyya.
Talatan–Mafara ya fadi haka ne da yake ganawa da Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya a Gusau.
Ya bayyana cewa jirgin farko ya sauka a tashar jiragen saman Sultan Abubakar III dake jihar Sokoto da karfe tara na safiyar Alhamis dauke da alhazai 552.
” Jirgin farko ya kwaso alhazan kananan hukumomin Bukkuyum, Birnin-Magaji, Kaura-Namoda, Zurmi da Tsafe.
Talata-Mafara ya ce bisa ga tsarin da suka yi jirgi na biyu zai taso daga Saudi ranar Alhamis sannan sauran alhazan da suka rage za su dawo gida ranar Asabar.
Discussion about this post