Jiya Laraba ne Gwamnatin Tarayya ta soke takardar iznin zama Najeriya da aka bai wa wasu kwararrun ma’aikatan kamfanin INTEL’S Nigeria Limited, da wasu kamfanoni biyar. INTELS dai mallakar tsohon mataimakin shugaban kasa ne, kuma jigo a jam’iyyar APC, wato Atiku Abubakar.
Hukumar Shige-da-fice ta Nijeriya, ta bayyana sunayen sauran kamfanonin da korar ta shafa, sun hada da PREDECO International Limited, West AFRICA Monetary Services Limited, Net Global System, MGM Logistics Solutions Limited ada kuma ORIEN Investment.
Ma’aikatan da korar da ritsa da su a cikin kamfanonin shida, an ba su makonni biyu, zuwa nan da 30 Ga Nuwamba da su tattare komatsan su su fice daga Najeriya. Idan ba haka ba kuwa, to za a yi musu mokar-kare a bisa umarnin Ministan Harkokin Cikin Gida.
Babban Kwantirola na Shige-da-fice, Muhammad Babandede, shi ne ya bayyana wannan soke takardar iznin zama da aka yi musu a Abija ta bakin kakakin yada labaran hukumar, Sunday James.
Ya na mai karawa da cewa dokar kasar nan ta sashe na 39, karamin sashe na 1 daga cikin dokar shige-da-fice ta 2015 a shashe na 5 karamin sashe na 5 ne ya bada ikon yin korar.
Discussion about this post