Annobar cutar korona ta yi mummunan tasiri ga tattalin arziki a duniya, ta yadda kuma ta riƙa yi wa mutane kisan-kiyashi a daidai lokacin da ake ta gaganiyar yadda za a daƙile annobar.
Sai dai kuma an ɗauki shekaru bayan ɓarkewar cutar, inda a yanzu a duniya ake addu’ar kada Allah maimaita afkuwar wannan annoba, wadda ake ganin ba a taɓa yin mai irin munin ta ba, to sai kuma tattalin arzikin ƙasashe a faɗin duniya ke ƙara fuskantar gagarimar matsalar taɓarɓarewa.
Tsayawa cak da masana’antu su ka yi a duniya, suka daina sarrafa kayan buƙatu na dole da na tafiyar da rayuwar yau da kullum a lokacin korona, ya ƙara azalzala matsalolin da su ne dai su ka riƙa bibiyar ƙasashen duniya har aka shiga mawuyacin halin da ake ciki a yanzu na tsadar Rayuwa.
Abin mamaki, nahiyar Afirka ba ta tagayyara da cutar korona kamar sauran nahiyoyin duniya ba, kamar yadda wasu suka riƙa yin kintacen cewa cutar za ta fi illata Afrika da farko.
To sai dai kuma a halin yanzu bayan wucewar cutar korona, yankin Afrika ne ya fi sauran nahiyoyi afkawa cikin matsanancin raɗaɗin tsadar rayuwa.
Farashin kayan abinci da kayan masarufi ya yi tashin da bai taɓa yi a baya ba, a ƙasashen Afrika masu ɗan karsashin tattalin arziki, irin su Sanagal, Sudan, Kenya, Afrika ta Kudu, Ghana da Najeriya.
Rashin aikin yi ga matasa a yankin ya haifar da ƙarancin samun sukunin yin hada-hadar kuɗaɗe ga matasa.
Ƙarin wata gagarimar matsala a yankin ita ce matsalar rashin tsaro wadda ta ke tilasta mutanen karkara yin hijira zuwa cikin birane. Kuma har yanzu an kasa daƙile wannan babbar matsala a Afrika ta Yamma.
A Najeriya matsalar da zama goma da ashirin. Ga dai matsalar rashin aiki, wadda ke tafiya kafaɗa da kafaɗa da tsadar rayuwa da tsadar kayan abinci da na masarufi.
A gefe ɗaya kuma kamfanonin ƙasashen waje sai ƙara nesa-nesa da Najeriya suke yi, su na fargabar zuba jari. Waɗanda kuwa suka rigaya sun ginu a cikin ƙasar, sun shiga tunanin ko dai su rage ma’aikata, ko kuma su rufe masana’antun kwata-kwata.
To ko da daɗi ko ba daɗi dai, nauyin samar da mafiya ya rataya ne a wuyan gwamnati. Ƙasashe irin su Brazil, Chile, Gungun Yankin Turai, Hungary, New Zealand, Norway, Peru, Poland, Birtaniya, Amurka da Koriya ta Kudu duk mun ga yadda Manyan Bankunan su su ka ƙara kuɗin ruwa, domin taushe barazanar ƙarin farashin kayayyaki.
Amma a daidai wannan lokacin, shi kuwa Babban Bankin Najeriya (CBN), sai ma ya karya ƙa’idojin da ya gindaya wa kan sa da kan sa, ya riƙa buga buga kuɗi domin biya wa Gwamnati buƙatar yawan ciwo wa ƙasa bashi.
Tabbas yawan basussukan da aka riƙa ciwowa ba tare da ana amfani da kuɗaɗen wajen yin abin da zai kawo wa ƙasa riba ba, shi ne ya ƙara dulmiyar da ƙasar nan cikin ƙuncin raɗaɗin tsadar rayuwa, saboda durƙushewar tattalin arziki.
Dalili kenan farkon abin da Gwamnatin Tinubu ta fara yi, shi ne ƙoƙarin ɗora wa doki sirdi, domin yin sukuwar zaburas da tattalin arziki.
Sai dai abin takaici, maimakon a ɗora sirdin a kan ɗanfilinge, danda ko akawal, sai aka ɗaura sirdin a gadon bayan makahon doki.
Hakan ya sa maimakon a samu sauƙi, sai ma aka ƙara danƙara wa talakawa da marasa galihu raɗaɗin tsadar rayuwa, ta hanyar ƙara farashin fetur, faɗuwar darajar Naira, dama kuma su na fama da masifar fitinrinun matsalar tsaro, musamman a yankunan karkara.
Irin kallon-kurar-Ƙosau ɗin da Buhari ya yi wa matsalar Najeriya, ta sa ya shafe shekaru takwas ya na gaganiya, amma bai iya magance komai ba.
Don haka kada ita ma Gwamnatin Tinubu ta ce za ta tura talakawa su shiga kogo su kamo mata maciji ba tare da cin maganin dafin maciji ba. Saboda ita ma Gwamnatin, ba maganin kawar da dafin macijin gare ta ba.
To ko da daɗi ko ba daɗi dai, nauyin samar da mafiya ya rataya ne a wuyan gwamnati. Ƙasashe irin su Brazil, Chile, Gungun Yankin Turai, Hungary, New Zealand, Norway, Peru, Poland, Birtaniya, Amurka da Koriya ta Kudu duk mun ga yadda Manyan Bankunan su su ka ƙara kuɗin ruwa, domin taushe barazanar ƙarin farashin kayayyaki.
Amma a daidai wannan lokacin, shi kuwa Babban Bankin Najeriya (CBN), sai ma ya karya ƙa’idojin da ya gindaya wa kan sa da kan sa, ya riƙa buga buga kuɗi domin biya wa Gwamnati buƙatar yawan ciwo wa ƙasa bashi.
Tabbas yawan basussukan da aka riƙa ciwowa ba tare da ana amfani da kuɗaɗen wajen yin abin da zai kawo wa ƙasa riba ba, shi ne ya ƙara dulmiyar da ƙasar nan cikin ƙuncin raɗaɗin tsadar rayuwa, saboda durƙushewar tattalin arziki.
Dalili kenan farkon abin da Gwamnatin Tinubu ta fara yi, shi ne ƙoƙarin ɗora wa doki sirdi, domin yin sukuwar zaburas da tattalin arziki.
Sai dai abin takaici, maimakon a ɗora sirdin a kan ɗanfilinge, danda ko akawal, sai aka ɗaura sirdin a gadon bayan makahon doki.
Hakan ya sa maimakon a samu sauƙi, sai ma aka ƙara danƙara wa talakawa da marasa galihu raɗaɗin tsadar rayuwa, ta hanyar ƙara farashin fetur, faɗuwar darajar Naira, dama kuma su na fama da masifar fitinrinun matsalar tsaro, musamman a yankunan karkara.
Irin kallon-kurar-Ƙosau ɗin da Buhari ya yi wa matsalar Najeriya, ta sa ya shafe shekaru takwas ya na gaganiya, amma bai iya magance komai ba.
Don haka kada ita ma Gwamnatin Tinubu ta ce za ta tura talakawa su shiga kogo su kamo mata maciji ba tare da cin maganin dafin maciji ba. Saboda ita ma Gwamnatin, ba maganin kawar da dafin macijin gare ta ba.
Discussion about this post