Mai Girma Gwamna, a yau jihar Jigawa tana fuskantar masifa ta ambaliyar ruwa wanda ba taba fuskanta ba a wannan shekaru.
Mai Girma Gwamna, a yau Jigawa ta Arewa Maso Gabas da Jigawa ta Arewa maso Yamma, yankin da ka fito ambaliya ta raba su da babban birnin Jaha Dutse.
A yau mutumin Hadejia bashi da hanyar zuwa K/Hausa, Guri, Gujungu ko Katagun.
Mai Girma Gwamna, bisa girmamawa ina tunasar da kai cewa, mutanen Jigawa sun zabe ka ne bisa amanar zaka kare musu rayukan su da dukiyoyin su.
Maigirma Gwamna ka tuna ka dau wannan alkawari, har kayi rantsuwa da Alkura’ani mai girma.
Duk da mun san cewa kujerar gwamna na nan, kuma ni na yaba da kokarin makaddashin gwamna a kokarin sa na kawo wa alummah, musamman wanda wannan masifa ta sama ta shafa tare da sauran hukumomi.
Mai Girma gwamna duk da haka babu lokacin da ya dace ka sakawa talakawan ka, ta hanyar nuna musu kauna da tausayi a yanayin da suka sami kansu da ya wuce wannan lokaci.
Mai Girma Gwamna babu wani abu da ya kai muhimmancin ka kasance a cikin talakawan Jigawa a yanzu, duba da irin ibtila’in da suke ciki yanzu.
Mai girma gwmna, wasu kaukan fa sun ta shi ba suma san ina za su dosa ba.
Mai Girma Gwamna, mutane fa dewa sun mutu sanadiyar kifewa a kwalekwale don neman tsira.
Mai Girma Gwamna, dubban gonaki fa ruwa ya shanye su, a yanzu fa mutane ta rai a ke bata gona ba.
Mai Girma Gwamna ya kamata ka yanke hutu, kazo kaga halin da mutanen da Allah ya baka amana suke.
YAWAN AMABALIYAR RUWA: Shin Lokacin Amfani da Shawarar Kwararrun Majalisar Dinkin Duniya Baiyi ba na Canja wa Hadejia Matsuguni?
Koda yake, dama kamar yadda tarihi ya nuna an kafa Hadejia ne, a cikin Tafkin Chadi, wurare irin su Hadejia na cikin yankin tafkin Chadi da ya kafe.
Inda za a ce Tafkin Chadi zai koma yadda ya ke a baya da tabbas ba za a samu garuruwa irin su Hadejia, Birniwa, Kiri Kasmma da dubban kauyukan su ba.
Kusan a wannan shekarun da duniya baki daya take fama da matsalar dumamar yanayi da chanjin yanayi, yankin Hadejia ba a barshi a baya ba wajen fuskantar wannan matsalar.
Kusan a yanzu duk lokacin da a ka samu masifar ambaliyar ruwa, ana asarar rayuka masu yawa, ga asarar gonaki da gidaje da kuma dukiya mai tarun yawa.
Abin mamaki kullun barazanar ambaliyar ruwannan karuwa ta ke yi, haw hawa take yi, ta bana tafi ta bara.
A shekara ta 2020 a tskanin watan Augusta zuwa October, ambaliyar ruwa ba karamar barna ta yi ba, kama daga asarar rayuka da dukiyoyi, wannan ambaliya har tayi barazanar tada Birnin Hadejia.
Majalissar Dinkin Duniya a binciken ta karkashin Group on Earth Observation (GEO), “sakamakom duba na tauraron Dan Adam a kan chanjin yanayi, alkaluma sun nuna cewa, a nan da shekaru biyu masu zuwa a kwai yiyuwar samun gaftarewar kasa a garuruwan Auyo, Birniwa da Hadejia”.
Kamar yadda daya daga cikin wakilan Majalissar Dinkin Duniyar a fannin Chanjin Yanayi Mr. Nura Jibo ya fada kamar a shekara ta 2020 “…matsalar Hadejia da ban take, ita Hadejia ta fado ne a kasan Hadejia Jama’are River Basin da kuma Kwamadugu Wetland, da ma garin (Hadejia) ya na kan hanyoyin da ruwa ya ke kangarawa zuwa Lake Chard” ya kara da cewa “babu wata dabara da ta ragewa mutanen wannan yaki, face tunanin chanja matsagunni”
Duk da kasancewar akwai shawarwari da aka bada, musamman mutanen wannan yankin a kan su yawaita dasa bishiyoyi, amma kokarin a wannan fannin yayi karanchi.
A wannan shekarar ma fa, barazanar wannan ambaliyar tafi ta wadda ta gabata, domin tun kafin a ce ruwan ya gama zuwa, kauyuka da dama sun tashi, a wasu wuraren an samu asarar rayuka, gonaki da dama ruwa ya shanye su, dubban mutane sun bar gidajen su, a wannan karon hatta makarantun gwamanti ma ruwa ya ci su.
Lokaci yayi fa, da masu fada a ji da hukumomin gwamnati ya kamata su sake bibiyar wannan ruhoton don yin abin da ya kamata.
Mutanen Hadejia ya kamata ku soma yin tunanin yin taswirar sabon birnin Hadejia a arewacin Hadejia, dama an ce turawan Ingila da suka zo sun bada wannan shawara.
alhajilallah@gmail.com
Discussion about this post