A sabuwar binciken kwakwaf da ya bayyana an bankado jerin sunayen wasu gaggan ‘yan Najeriya dake da hannu dumudumu wajen taya tsohon shugaban Najeriya, Janar Sani Abacha harkallar biliyoyin daloli daga asusun gwamnatin Najeriya suka kimshe su a bankunan kasashen waje.
A watan Mayu an abnkado wasu tarin kudade har Dala miliyan $23.5 wanda a ka jibgesu a asusun kasdar Birtaniya da sunan tsohon janar din.
PREMIUM TIMES ta samu sahihan bayanai da takardu dake nuna yadda wasu ‘yan Najeriya suka taya shugaban mulkin sojan watandar kudaden kasa sannan da kimshe su a Asusun bankunan kasashen turai da na Amurka ta hanyar yaudara, yankan baya da zuka kudaden kwangilolin karya don wafce biliyoyin naira da dala da jida su a awadanan asusu.
Kamar yadda aka gani a wasu takardun bincike da suka nuna yadda tsohon mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Ismaila Gwarzo a wancan lokaci ya kirkiro wasu dalilai na karya, wanda ya sa aka zaftare akalla dala biliyan $2 wai don yin wasu ayyukan samar da tsaro na gaggawa. Haka dai babu aikin taro ballantan na sisi, aka yaudari Najeriya karkashin Gwamnan babban bankin kasa a wancan lokacin Paul Ogwuma Abacha da Gwarzo suka wafce wadannan kudade suka kama gaban su. Kamar yadda gwamnatin Amurka ta fitar.
Maimakon a yi amfani da kudin wajen ayyukan samar da tsaro kamar yadda akanuna hakan ne dalilin cire su sai kawai wasu daga cikin makarraban Abacha da suka hada da babban dan sa Mohammed Abacha da Gwamnan Kebbi, Abubakar Bagudu suka karkatar da kudin suka jibge su a Asusun bankunan waje.
Daga 1998 zuwa yanzu, an kwato sama da dala biliyan $3.6 daga kasashen waje na wasu daga cikin kudaden da Abacha yayi harkallarsu a lokacin yana shugaban Najeriya.
SUNAYE
1 – Gabriel Katri:Katri dan asalin kasar Swss-Isreali kuma kwararren ma’aikacin banki wanda yake harkallar hadadar shige da ficen kudade wa shugabannin kasashen Afrika da na kasashen Larabawa. kotu ta taba daure shi bayan kamashi da laifin harklallar kudade.
2 – Gilbert Chagoury
3 – David Umaru – Shine mai baiwa Abacha da iyalan sa shawara kan harkokin shari’a
3. Abubakar Bagudu – Gwamnan jihar Kebbi, kuma shine gogarman da kusan a kowani lokaci aka bankado harkallar Abacha sai an ga da hannun sa dumudumu a ciki. ko a wajen jigilar kudaden ko kuma kimshe a asusun bankunan kasashen waje.
5. Danilo Djuroiv
6. Ahmadu Daura
7: Mark Risser
8. Jean-Pierre Decker
9. Richard Granier-Deffere
10. Raj Arjandas Bhojwani
11. Anthony Ani
12. Ismaila Gwarzo
13. Dan Etete
14. Buba Marwa
15. Paul Ogwuma
16. Mohammed Abacha
17. Abba Abacha
18. Maryam Abacha
Discussion about this post