Idan ba a manta ba a shekarar 2017 shugaban ƙasa Muhammadu Buhari yayi ikirarin cewa gwamnatin sa za ta gyara cibiyoyin kiwon lafiya 10,000 a fadin kasar nan.
Kamar yadda ya fadi za ta gyara cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko uku a kowace jiha da Abuja kenan.
Gwamnati ta ce za ta iya gyara cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko 109 a kasar nan saboda karancin kudi.
A watan Disembar 2017 gwamnati ta bude asusun naira biliyan 28 domin inganta cibiyoyin kiwon lafiya a kasar nan.
A lokacin tsohon Minista Isaac Adewole ya ce za a fara aiki da kudin asusun a shekarar 2018.
A watan Disembar 2018 shugaban hukumar kula da cibiyoyin kiwon lafiya ta ƙasa NPHCDA Faisal Shu’aib ya ce gwamnati ta gyara cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko guda 4,000 a kasar nan.
Wakiliyar PREMIUM TIMES ta samu sunayen cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko guda 109 da gwamnati ta zaba domin ta gyara saboda lalacewa da suka yi.
An ziyarci wasu daga cikin cibiyoyin kiwon lafiyan da gwamnati ta ce ta gyara a jihohin Borno, Nasarawa, Ebonyi, Ondo, Kano, Benue, Niger da Kaduna inda ta ga babu gyarar da aka yi a asibitocin.
Cibiyar kiwon lafiya na matakin farko dake Katanmi a jihar Sokoto
Wakiliyar PREMIUM TIMES ta ce ta ziyarci cibiyar kiwon lafiya a matakin farko dake Katanmi a watan Satumba 2021 inda ta iske tarin ruwa kaman rafi a kofar shiga asibitin.
Da kyar wakiliyar ta samu shiga asibitin saboda lokacin damina ne sannan babu hanya mai kyau.
Cibiyar lafiya dake Katanmi na fama da matsalolin da suka hada da karancin ma’aikata, karancin kayan aiki, karancin katifu da gadaje.
Sannan kuma akwai matsalar kwantar da marasa lafiya, rashin ruwa, rashin wutan lantarki, rashin janareta, rashin motan dauka marasa lafiya da dai sauran su.
Da yake tattaunawa da PREMIUM TIMES shugaban asibitin Mohammed Mohammed ya ce kungiyar kananan hukumomin ta Najeriya ALGON ta gina cibiyar lafiyan a shekarar 1999 sannan a lokacin mulkin tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan aka gyara asibitin.
Mohammed ya ce tun daga wannan lokacin asibitin ba ta sake samun gyara ba duk da alkawarin gyara dagwamnatin Buhari ta rika yi.
Ya ce a shekarar 2012 kungiyar ALGON ta siyo janareta wa asibitin amma tun da janaretan ya lalace a 2016 asibitin take cikin duhu da rashin ruwan fanfo.
Shugaba mai kula da sashen haihuwa Mariam Umar ta ce zazzabin cizon sauro kawai na yin ajalin mata masu ciki akalla 25 duk shekara a kauyen.
Ta ce mata masu ciki na yawan kamuwa da zazzabin cizon sauro wanda ke cutar da lafiyar su musamman wajen haihuwa.
Daga nan wani ma’aikacin asibitin Buhari Mohammed ya koka da yadda mutane ke yawan kamuwa da cutar amai da gudawa a kauyen.
Mohammed ya ce duk shekara cutar ta na yin ajalin mutane da dama a kauyen.
Ya ce hakan na da nasaba da rashin samun tsaftacen ruwa da yadda mutane ke gina rijiya kusa da dakin bahaya.
Cibiyar lafiya dake Dange Shuni
Shugaban cibiyar lafiya na matakin farko dake Dange Shuni Mustapha Alkali ya ce hukumar NPHCDA ce ta gina asibitin a shekarar 2007 a karamar hukumar Dange Shuni sannan aka gyara asibitin a shekarar 2018.
Asibitin na fama da matsalolin da suka hada da rashin ingantacen wurin aiki, rashin kayan aiki, rashin isassun ma’aikata, rashin biyan ma’aikata albashi da dai sauran su.
Alkali ya ce zaman su a asibitin na jefa rayuwar ma’aikata da marasa lafiya cikin hadari saboda yadda ginin asibitin ke rushewa.
Ya ce zuwa yanzu ssibitin bata da dakin kwantar da maza da dakin yi wa mata awo saboda duk sun fadi.
Bayan haka Alkali ya ce asibitin na fama da karancin ma’aikata.
Sakataren hukumar cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko na jihar Sokoto PHCDA Adamu Romo ya ce hakkin ma’aikatar kiwon lafiya ta jiha ne ta gyara cibiyoyin kiwon lafiyan da ke kauyuka a jihohi.
Discussion about this post