Jam’iyyar APC ta amince da zaɓen Sanata Abdullahi Adamu sabon Shugaban Jam’iyya ba tare da jefa ƙuri’a ba.
An zaɓe shi ne bayan da sauran ‘yan takara su ka janye masa, a matsayin sa na wanda ya fi kwanta wa Shugaba Muhammadu Buhari a ran sa.
Adamu wanda tsohon ɗan PDP ne, ya shafe shekaru takwas ya na gwamna a Jihar Nasarawa ƙarƙashin PDP, tsakanin 1999 zuwa 2007.
Adamu ya shiga Majalisar Dattawa inda ya taka rawar neman Obasanjo ya zarce, yunƙurin da bai yi nasara ba.
Bayan saukar sa Gwamna, EFCC ta kama shi har ta nemi ya yi aman naira biliyan 15.
Lokacin da Adamu ke Gwamnan Nasarawa a matsayin ɗan PDP, shi ne Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF),
A Majalisar Dattwa ya zama Shugaban Ƙungiyar Majalisar Dattawa ‘Yan Arewa. Sai dai an tsige shi bayan da aka gano ya wawure wasu maƙudan kuɗaɗe.
Ya samu shiga wurin Shugaba Muhammadu Buhari tun a cikin 2015, inda a Majalisar Dattawa ya zama gogarman Shugaba Buhari, mai ragargazar Shugaban Majalisar Dattawa na lokacin, Sanata Bukola Saraki.
Omisore A ‘Next Level’: Yadda Ya Zama Mataimakin Shugaban APC Shekara Ɗaya Bayan Ya Shiga Jam’iyya Mai Mulki:
Iyiola Omisore ne aka zaɓa matsayin sakataren jam’iyyar APC, bayan ya doke tsohon Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Ken Nnamani da Yakubu Dogara, tsohon Kakakin Majalisar Tarayya.
Nnamani da Dogara duk tsoffin ‘yan PDP ne su ma. Omisore kuwa kafin ya koma PDP, ya yi Mataimakin Gwamna a Jihar Osun, ƙarƙashin jam’iyyar AD. Daga baya ya fice ya koma PDP.
Cikin Fabrairu 2021 ya canja sheƙa zuwa APC. Amma ana raɗe-raɗin cewa an saka masa ne da kujerar Matakimakin Shugaban APC saboda rawar da ya taka har APC ta kayar da PDP a zaɓen Gwamnan Osun cikin 2018, inda har Gboyega Oyetola ya zama Gwamna a 2018.
A zaɓen, PDP ke kan gaba, APC ta biyu sai Omisore na uku a ƙarƙashin SDP. INEC ta ce zaɓen bai kammalu ba, sai da aka sake zaɓe a wata rumfa.
Yayin da APC da PDP su ka fahimci cewa Omisore ba zai iya yin nasara ba, jam’iyyun biyu sun riƙa zawarcin sa domin ya umarci magoya bayan sa su zaɓi ‘yan takarar su.
Daga ƙarshe dai Omisore ya ce magoya bayan sa su zaɓi APC. Bayan Oyetola na APC ya yi nasara, shi kuma Omisore ya canja sheƙa ɗungurugum ya koma APC cikin 2021.
Sai dai kuma Adamu da Omisore za su hau kujera mai zafi, domin tun a farkon hawan su za ci gadon shari’a a kotu, wadda PDP ta kama APC ƙara, ta na neman a soke rajistar APC, a hana ta shiga zaɓen 2023, kuma a haramta taron gangamin da ya kai ga zaɓen su Abdullahi da Omisore a matsayin shugabannin APC.
Discussion about this post