A ranar Juma’ar da ta gabata ne Amurka ta saka wasu ‘yan Najeriya shida cikin jerin sunayen ‘yan kasar da aka kebe na musamman da kuma wadanda aka kyamata saboda tallafin da suke baiwa kungiyar Boko Haram.
A cewar wata sanarwa da kakakin ma’aikatar harkokin wajen Amurka Ned Price ya fitar, “Ma’aikatar Baitulmali ta Amurka ta kara da cewa wasu ‘yan Najeriya masu suna kamar haka; Abdurrahman Musa, Salihu Adamu, Bashir Yusuf, Muhammed Isa, Ibrahim Alhassan. da Surajo Muhammad na cikin jerin sunayen ‘yan kasa na musamman da aka kebe kuma aka sa wa ido da kyamata saboda hannu da suke dashi a harkokin Boko Haram”.
An saka sunayen ‘yan Najeriya 6 da ake zargi da ba da kudaden ayyukan kungiyar ta’addanci ta Boko Haram, wadanda a kalla shekaru 10 da suka gabata ke haddasa rashin tsaro a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya da ma wasu kasashe makwabta.
Ayyukan kungiyar sun yi sanadin mutuwar mutane sama da 100,000 a Arewacin Najeriya tun daga shekarar 2009, kamar yadda alkaluman hukuma suka nuna.
Kamar yadda rahoton Daily Trust ya ruwaito, kotun daukaka kara ta birnin Abu Dhabi da ke kasar Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) ta yanke wa mutane 6 hukuncin dauri kan zargin bayar da kudade ga kungiyar ta’addanci.
Biyu daga cikin wadanda aka yankewa hukuncin, Surajo Muhammad da Salihu Adamu, an yanke musu hukuncin daurin rai-da-rai yayin da sauran hudun, Ibrahim Alhassan, AbdurRahman Musa, Bashir Yusuf da Muhammad Isa aka yanke musu hukuncin daurin shekaru 10 kowannensu.
Har yanzu dai Najeriya na fama da ayyukan ta’addanci na Boko Haram. Baya ga Boko Haram akwai kuma ƴan ta’adda da duka gallabinyanikn Arewa Mago Yammacin kasar.
Discussion about this post