Gogarman ‘yan Bindiga, Bello Turji, a wata wasika da ya rubuta zuwa ga shugaban Kasa Muhammadu Buhari da Gwamna Bello Matatwalle na Jihar Zamfara da Sarkin Shikafi ya bukaci a zauna lafiya kamar Yadda ake zaman lafiya a can baya.
Turji ya bayyana cewa ana zaluntar Fulani da kuma nuna musu banbanci a harkar rayuwa ta yau da kullum.
A wasikar Turji yace kashe-kashen da ake yi na Al’umma wadanda basu ji ba basu gani ba zai zo karshe.
Yace Yan Bindiga sun kashe Yan sa Kai da Jami’an Tsaro suna kuma dauki mutane domin karbar kudin fansa, yace insha’Allahu za’a kawo karshen shi da yardar Allah mutukar za’a soke kungiyoyin ‘Yan Sakai zamu mika kanmu da makamanmu.
Matukar aka kawar da kabilanci da ake nuna mana (Fulani) da son rai zamu dawo mu zama abu daya kamar Yadda muke da a can baya, uwa daya uba daya (Hausa-Fulani) kuma mu yafewa juna bisa ga kaddarar Allah.
A cikin wasikar Turji yace suna “Akwai bukatar zama da sarakunan kasar Zamfara da kuma manyan malamai, idan hakan ta samu ni Muhammadu Bello Turji Kacalla nayi alkawarin harga Allah zan karbi duk Bindigogin da ake ta’addanci da su in mika su ga hukumomin Najeriya mutukar gwannatin zatayi mana adalci da kula da sauran Jama’ar kasa kuma a bar cin zarafin Fulani.
Bamu fada da gwannati, kuma ba wani kasa muke son kafawa ba, kuma ba mulki muke nema ba, ba wata kungiya muke son kafawa ba. Abubuwan da ake yiwa Fulani a kasar nan, na cin zarafin Fulani da nuna musu banbanci ko a cikin kasuwanni da kuma cikin Garuruwa shi ya haddasa wandanan abubuwa na rashin zaman lafiya.
Kada a yaudaremu, kuma kada a yi mana zagon kasa, muyi don Allah, kuma don kasarmu ta zauna lafiya kamar yadda muke a can baya. Kowa ya tsaya a wurinsa mu bar jami’an tsaro suyi aikinsu yadda suka saba a kuma hukunta mai laifi ba tare da nuna wani banbanci ba. Insha Allahu baza’a sake ganin bindiga ba sai ga jami’an tsaro kamar yadda aka saba gani.
Abu na karshe a hada sarakuna da malaman addinin Musulumci kuma muna bukatar ganin Sheikh Ahmad Gumi wajen zaman da za’a yi na kawo karshen wannan ta’addanci domin shi muka sani domin ya taba kawo mana ziyara.
Kuma Sheikh Gumi yayi mana wa’azi, kuma yanzu munga amfanin wa’azin don haka muna son kasarmu ta zauna lafiya da yardar Allah.
Dalilin rubuta wasika
Murtala Rufa’i, masanin tarihi a jami’ar Usman Danfodiyo dake Sokoto, ya shaidawa PREMIUM TIMES cewa Turji ya rubuta wasikar ne saboda wasu dalilai guda biyu.
Malam Rufa’i wanda shi ne marubucin litaffin nan mai suna ‘Ni Dan Bindiga ne’ (Iam a Bandit) yace Turji ya fuskanci bore daga wasu Yan Bindiga bayan kone matafiya a cikin motar bas a Karamar Hukumar Sabon Birni dake Sokoto.
Wasu daga cikin shugabanin Yan Bindigar basu ji dadin matakin da Turji ya dauka ba wajen kone matafiya da yayi ba, sun bayyana hakan ne wajen taro da sukayi a ranar 13 ga watan Disamba inda suka nunawa Turji kuskurensa, cewar Malam Rufa’i.
Malamin yace a taron da akayi, Turji ya amince cewa matakin da ya dauka yayi kuskure.
Wasikar kamar wata hanya ce ta neman mafita daga abinda yayi wanda abokansa na ta’adanci basu ji dadi ba. Kuma ya samu labarin cewa sojoji suna shirin kawo masa hari, cewar Malam Rufa’i.
Discussion about this post