Sakamakon zaben kananan hukumomi da aka bayyana a Kano ranar Lahadi, shugaban hukumar zabe na jihar Kano, Ibrahim Garba-Sheka ya ce gaba daya kananan hukumomin jihar Kano 44 da kujerun kansiloli 484 duk APC ce ta cinyo su tas.
” Yan takara na jam’iyyar APC ne suka cinye zaben tas-tas. Duka kananan hukumomi 44 da kujerun kansiloli 484 duk APC ce ta lashe su tas, bata rage ko sidi.
Garba-Sheka ya zabe ya guna cikin lumana da kwanciyar hankali.
” Kuri’un da aka kada a zaben sun zarce miliyan biyu duk da ko ana ci gaba da karkare sauran ayyukan da ba a rasa bana zaben.
Sai dai kuma duk da wadannan nasarori da aka samu a wannan zabe da aka gudanar, kamar yadda Garba-Sheka ya karanto su, jam’iyyar PDP bangaren tsohon gwamna Rabiu Kwankwaso ta janye daga fafatawa a wannan zaben.
Hakan bai hana bangaren PDP na Aminu Wali shiga zaben ba, sai dai ko Kansila daya cikin kansiloli sama da 400 da aka zaba basu ci ba.
Discussion about this post