“Baka san ni shafaffe da mai bane, za ka wani ce in bi dokar lafiya” daga nan sai tsohon gwamna AbdulAziz Yari ya bangaje wannan jami’in lafiya yayi tafiyar sa.
Hukumar kula da filayen jiragen sama ta kasa ta koka kan yadda tsohon gwamnan jihar Zamfara AbdulAziz Yari ya nemi aikata dabanci a filin jirgin saman Aminu Kano kawai don jami’in lafiya ya umarce shi da ya bi dokar lafiya da aka saka a filayen jirgin.
FAAN ta shaida cewa tsohon gwamna Yari ya ki bin dokokin da aka saka a tashohin filin jiragen saman Najeriya na dakile yaduwar Korona, kamar yadda kowa yake bi.
” Irin abinda Yari yayi bai dace da wani shugaba ba, musamman ganin sune ya kamata ace ana koyi da su ba su rika karya doka ba yadda suke so kuma su nuna ba a isa a ce musu komai,
Hukumar ta kara da cewa, ” jami’in ta ya umarce shi ne da ya dan dakata ayi wa jakar sa feshi kamar yadda aka saba yi wa kowa da kowa kafin ya shiga jirgi. ” juyawar sa ke da wuya sai ya bangji jami’in ya ce ba za ayi masa b, daga nan sai ya kama gabn sa kawai yayi tafiyar sa.
Discussion about this post