Hukumar NCDC ta sanar da karin mutum 328 da suka kamu da cutar Coronavirus a Najeriya ranar Juma’a.
Alkaluman da hukumar NCDC ta fitar ranar Juma’a, sun nuna cewa Jihar Legas ta samu karin mutum 131, FCT – 70, Bauchi – 25, Rivers – 18, Oyo – 16, Kaduna – 15, Gombe – 14, Edo – 12, Ogun – 13, Jigawa – 8, Enugu – 6, Kano – 5, Osun – 2, and Ondo – 2
Yanzu mutum 11,844 suka kamu da cutar a Najeriya, mutum 3696 sun warke, 333 sun mutu.
Duk da yawan mutane da ake samu sun kamu da cutar a kullum a Najeriya, wasu da dama na ganin har yanzu ba a yi wa mutane gwajin cutar yadda ya kamata a kasar.
Jihar Legas na ci gaba da samun daruruwan mutanen da suka kamu da cutar Korona babu kakkautawa.
A ranar Juma’a kawai, jihar Legas ta samu karin mutum sama da 130.
Har yanzu dai jihar Legas ne ke da mafi yawan wadanda suka kamu da mutum 5, 663 cases, followed by Kano – 985, FCT – 862, Katsina – 385, Edo – 364, Oyo – 334, Kaduna – 335, Borno – 322, Ogun – 329, Jigawa – 282, Rivers – 308, Bauchi – 281, Gombe – 184, Sokoto – 115, Kwara – 127, Plateau – 113, Delta – 116, Nasarawa – 90, Zamfara – 76, Ebonyi – 80, Yobe – 52, Osun 49, Akwa Ibom – 45, Adamawa – 42, Niger – 41, Imo – 47, Kebbi – 33, Ondo – 38, Ekiti – 25, Enugu – 30, Bayelsa – 30 Taraba – 18, Abia–15, Benue – 13, Anambra – 12, and Kogi – 3.