• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

WALLE-WALLE: Yadda mutumin da SARS suka kama shekara biyar baya, ya bace ko sama ko kasa

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
December 6, 2018
in Babban Labari, Rahotanni
0
SARS Police Abuja

SARS Police Abuja

Ba a banza jama’a da dama ke korafi da kiraye-kirayen a yi wa rundunar ‘yan sandan kai daukin gaggawar dakile fashi da makami, wato SARS, kwaskwarima ba. Wasu ma cewa su ke yi a ruguza rundunar kawai.

Bari mu dauki labarin abin da ya faru da Oluwaseyi Adesuyi, wanda jami’an SARS suka kama. Rabon da a ji labarin inda ya ke ko halin da ya ke ciki, tun a ranar 15 Ga Yuli, 2013, lokacin da SARS suka gabatar da shi a gaban ‘yan jarida, bisa zargin sa da ake yi da laifin garkuwa da mutane.

Tun daga ranar, har yau din nan, mutumin ya bace, babu labarin sa, an rasa inda ya ke.

SARKAKIYA

’Yan sanda, wadanda dama su ne suka kama shi, kuma suka gabatar da shi a gaban ‘yan jarida, sun kasa bayyana abin da ya faru da shi. Sun kasa gabatar da duk wani rubutaccen bayanin kama shi, ko yadda aka yi suka kama shi, ko ma inda suka kama shi. Bai dai tsere daga hannun ‘yan sanda ba, kuma babu wata hujja rarrauna ko kwakkwara da ke nuna cewa an gabatar da shi kotu, ballantana a ce ya na kurkuku a tsare.

NEMAN ADESUYI RUWA A JALLO

Iyalan Adesuyi sun yi ta neman maigidan na su a kowane ofishin ‘yan sanda a jihohin Lagos, Ondo, har da Abuja, amma ba su cin karo da komai, sai dai bayanin cewa ba a san abin da ya faru da shi ba.

LAIFIN DA AKE ZARGIN YA AIKIATA

Oluwaseyi, wanda bai kammala Babbar Kwalejin Ilmi ta Adeniran Ogunsanya, da ke jihar Ondo ba, sai ya daina karatun, ya na cinikin wayoyin hannu ne da kuma kananan kwamfutocin tafi-da-gidan-ka na laptops, a kasuwar Alaba da ke Lagos.

A cikin watan Yuni, ya na tuki a cikin unguwar Okokomaiko, Lagos, sai wasu da suka ce jami’an SARS ne, suka tare shi, kuma nan take suka kwace masa motar sa, samfurin Nissan Pathfinder SUV.

‘Yan sandan sun caje shi da cewa ya sayi kwamfuta laptop wacce aka sata daga wani mai suna Kehinde Bamigbetan, wanda a lokacin da aka ce an yi satar, ya na shugabancin karamar hukumar Ejigbo. Amma a yanzu Kehinde Kwamishina ne na Yada Labarai, a karkashin gwamnatin jihar Lagos.

Kehinde ya tsira daga wadanda suka sace shi, bayan ya yi kwanaki bakwai a hannun su tare da biyan diyyar kudade

INA OLUWASEYI YA KE NE?

Bayan kwanaki uku ba a ji labara ko duriyar Adesuyi ba, kuma wayar sa a kashe, sai abokan sa suka kira iyayen sa da ke zaune a Akure, domin su tambaya su ji ko su na da labarin dan su Adesuyi.

Iyayen sa sun damu matuka, kuma hankulan su ya tashi, inda mahaifin sa ya tashi ya bazama neman inda dan sa Oluwaseyi Adesuyi ya ke.

Ya yi ta neman sa a ofisoshin ‘yan sanda da ma wasu wurare da dama, har bayan kwanaki da yawa, amma babu labarin inda ya ke.

Mahaifiyar sa Elizabeth hankalin ta fa ya tashi, har ta rika sambatu ta na cewa: “Da irin wannan tashin hankali da na shiga a ciki, har gara ma a ce dan mutum mutuwa kawai ya yi.”

Ba ta dai hakura ba, ta yi ta addu’o’i har da azumi. A nan nan rannan sai addu’ar ta ta samu karbuwa.
Yadda aka yi kuwa, wani ne ya ba su shawarar cewa kamata ya yi a je ofishin SARS da ke Ikeja a bincika a gani ko za a dace idan ya na can.

AL’AJABI A OFISHIN SARS: Ga sunan wanda ake nema, amma babu shi

Suka kuwa je ofishin SARS, suka bincika. Aka dauko rajistar wadanda ake kamowa aka tsarewa, aka yi sa’a sai ga sunan sa a cikin littafin rajista.

Sai dai kuma maimakon a gabatar musu da dan su su yi ido da ido da shi, duk sai jami’an SARS suka yi turus, aka yi carko-carko!

“Mu ka tambaye su ina dan mu? Babu amsa! Me ya faru da shi? Babu amsa! Me ake ciki ne? Kowanen su ya yi shiru! Duk da haka ba mu hakura ba, mu ka rika zuwa ofishin a kullum. Mu dai ba mu gan shi ba. Amma tunda sun ce ya na hannun su doming a sunan sa mun gani a rajista, sai muka kaddara cewa ya nan da ran sa.” Inji Elizabeth.

Sun ce jami’in da batun dan su ke hannun sa, ana kiran sa ne da lakabin Jamaica. Ba su san sunan sa ba, domin babu mai kiran sa da sunan sa na ainihi, sai Jamaica. Kuma ba su sanya kakin ‘yan sanda ballantana a gane mukamin sa.

Sai dai kayan gida suke sa wa ko kuma bakar rigar nan ta aiki, mai dauke da sunan SARS.

“A karshe, sai suka ce mana wanda mu ke nema din nan, dan fashi da makami ne, don haka ba za mu iya ganin sa ba. Har yau kuma ba mu sake ganin sa a idon mu ba tun daga ranar da aka kama shi.” Inji Elizabeth.

YADDA WANI DAN SANDA YA DAMFARI IYAYEN OLUWASEYI

Makonni da dama bayan iyayen sa sun yi ta zuwa ofishin SARS ba tare da samun nasarar ganin dan su ba, sai wani mutum ya kira su a waya, ya ce masu a cikin kurkukun ‘yan sanda daya aka kulle shi da Oluwaseyi, amma ba laifi iri daya ake tuhumar su da shi ba.

Mutumin ya ce dama Oluwaseyi ne ya ba shi lambar iyayen na sa, ya ce idan ya fita daga hannun hannun ‘yan sanda, to ya kira su domin ya shaida musu halin da dan na su ke ciki.

Mutumin ya shaida wa Elizabeth, mahaifiyar Oluwaseyi cewa akwai wani jami’ain dan sandan da za su yi wa magana domin ya taimaka a sake shi.

“Mu ka kira lambar da ya ba mu, sai aka ce mana ai wayar da dan mu suka saida daga hannun dan fashi ya saye ta, kuma motar da dan na mu ya ke hawa, wai ita ma a hannun dan fashi ya saye ta.’’

Daga nan ta ci gaba da cewa wannan dan sanda bai bayyana kan sa ba, sai ma ya nemi a ba shi naira 200,000.00, domin ya taimaka a saki Oluwaseyi.

Ya ce sun nemi kudin sun ba shi, saboda su na so su ga dan su, su kuma ga halin da ya ke ciki. Sai dai kuma bayan da suka biya kudin, sai wannan dan sanda ya yi ta neman karin kudi a hannun su.

Yayin da suka ce masa ba su da hanyar samun wasu kudin da za su ci gaba da ba shi, sai ma ya daina daukar wayar su, ya rika yi musu walle-walle. Daga nan sai suka fahimci ya daina amfani da lambar wayar da suke kiran sa. Karshe ma sai suka gano cewa ya yi ritaya daga aikin dan sanda.

A SANAR DA NI HALIN DA DA NA KE CIKI -Elizabeth

Elizabeth ta na magana murya ta na rawa, ta yi rokon a taimaka a sanar da ita halin da dan ta ke ciki. Ta ce dan ta ba mai fitina ba ne, kuma shi ba barawo ba ne. Wayoyi ya ke sayarwa wadanda ake shigo musu da su ne daga China.

BA MU TASKACE SUNAYEN WADANDA MU KE KAMOWA – SARS

Yayin da wakilin mu ya ziyarci ofishin SARS da ke Ikeja, inda a can ne aka yi wa Oluwaseyi ganin karshe, an shaida masa cewa babu yadda za a yin ya iya sanin yadda ta karke da shi.

Shugaban SARS na Ikeja, Peter Gana, wanda Babban Sufurtanda ne, ya ce bai dade da kama aiki a wurin ba. Daga watan Yuli ya fara, kuma shi ne babban jami’i na biyar da aka yi a wurin tun 2013, bayan kama Oluwaseyi da ake magana.

“Ba zan iya taimakon ka dangane da abin da ka ke neman sanin ba, saboda ba ka da sunayen jami’an da ke aiki a lokacin da abin ya faru.” Inji Gana.

WALLE-WALLE A OFISHIN SARS

Da aka tambaye shi me zai hana ya bincika a cikin littafin da suke taskace bayanai da ranaku da shekaru, tunda sunan wanda ake zargin ya bace din na nan, sai Gana ya ce su wannan ofishi na su ba ya adana rekod na bayanan kamammun da ake tsarewa a caji ofis na su na SARS.

“Idan ma na dauke ka na kai ka inda ake adana bayanan, za ka ga ba kimtse suke ba. Komai a hargitse, wani a kan wani, kuma tarwatse a kan dabe. Wasu ma sun jike da laimar ruwa. Kai ko da ma mun ga takardun bayanan, to ina tabbatar maka ba za su iya karantuwa ba, domin ruwa ya jike rubutun yadda ba zai karantu ba.” Haka Gana ya shaida wa wakilin PREMIUM TIMES, yayin da ya je binciken kwakwaf a ofishin SARS.

Gana ya ci gaba da cewa shi kan sa ya koyi darasi, domin duk wani batu da ya shafe shi kai tsaye, to ya na yin kwafe guda na bayanan ya adana a gidan sa.

Sai ya ce ya na yin haka ne domin gudun kada bayanan su salwanta a yi ta kame-kame.

Har ma ya buga wa wakilin mu wani misali, ya ce an nemi wasu bayanai na abin da ya faru a cikin watan Fabrairu, 2018, aka rasa. Ya ce shi ya sanya tun daga lokacin ya shiga taitayin sa, ya rika yin kwafe na bayani ya na taskacewa a gida, saboda gudun tashin-tashina wata rana.

A karshe, shugaban SARS Gana na Ikeja, Lagos, ya shawarci wakilinmu da ya tuntubi Abba Kyari, domin shi ne shugaban SARS na wurin a cikin 2013. Shi ne ya fi dacewa yay i bayani dangane da inada Oluwaseyi ya ke.

Yayin da aka tambayi Abba Kyari, wanda a yanzu shi ne shugaban rundunar RRS, da Sufeto Janar Ibrahim Idris ya kafa, sai ya buga rantsuwa ya ce, “wallahi ba zan iya tunawa ba ko wane mutum ne ake magana a kai ba, domin abin ya dade. Amma me ya sa tun tsawon wancan lokacin ba su neme shi ba sai yanzu?

Tags: AbujaLabaraiNajeriyaNewsPREMIUM TIMESSARS
Previous Post

Mata sun ninka maza har sau uku a yawan adadin wadanda suka fi fama da ciwon kai – BINCIKE

Next Post

Ghali Na’abba ya fice daga APC

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Babu abin da Buhari ya tsinana wa Najeriya, ba zan yi shi ba – Ghali Na’abba

Ghali Na'abba ya fice daga APC

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Kano ta hana lika fastoci a ginegine a fadin jihar
  • Sojoji sun kashe ‘yan ta’adda 58, sun kama wasu 161 a cikin makonni biyu a yankin Arewacin Najeriya
  • Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa
  • SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Dalilin da ya sa INEC ta yi wa kotu jayayyar kwafe-kwafen bayanan da Atiku da Obi su ka gabatar – Lauyan INEC
  • HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.