• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Tambuwal and Atiku

    FIDDA-GWANIN PDP 2023: Tambuwal ya janye ya ce ya na bayan Atiku

    An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba  sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad

    An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad

    An yi amfani da ƴan daba ne aka kada ni – Bashir Ahmed

    An yi amfani da ƴan daba ne aka kada ni – Bashir Ahmed

    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Tambuwal and Atiku

    FIDDA-GWANIN PDP 2023: Tambuwal ya janye ya ce ya na bayan Atiku

    An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba  sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad

    An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad

    An yi amfani da ƴan daba ne aka kada ni – Bashir Ahmed

    An yi amfani da ƴan daba ne aka kada ni – Bashir Ahmed

    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Zaben Fidda Gwanin Jam’iyyar APC: Gaskiyar Abinda Yake Faruwa A Jahar Zamfara, Daga Imam Murtadha Gusau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
October 6, 2018
in Ra'ayi
0
APC Congresses

APC Congresses

Bismillahir Rahmanir Rahim

Ya ku Jama’ah! Duk wanda yake nesa ko kuma wanda bai san hakikanin abun da yake faruwa a jahar Zamfara ba game da badakalar da ta kunno kai a kan zaben fitar da Dan takarar fidda gwani na jam’iyya mai ci wato APC, zai yi ta maganganun da basu dace ba, har ta kai ga ya zalunci wasu saboda rashin sani, ko kuma ya rinka hango cewa ko gwamnan jahar wato Abdul’aziz Yari Abubakar yana da gaskiya a kan kumfar baki da tayar da jijiyar wuya da yake yi a kafafen yada labarai. Ko kuma mutumin da ya jahilci me ke faruwa ya dauka cewa bangaren gwamnan ake neman a zalunta saboda babatun da yake yi a kafar yada labarai. Alhali duk wannan ba haka bane, domin gaskiyar magana, tsakani da Allah, shine yake son ya zalunci al’ummar jahar Zamfara, ya danne su, ya hana a basu hakkin su na jefa kuri’a da kundin tsarin mulkin kasar mu Nigeria ya basu, ya kakaba masu Dan takarar da basu so da karfi da yaji.

Imam Murtada Gusau
Imam Murtada Gusau

Jama’ah da farko abinda nike son ku fahimta shine, wallahi, wallahi, wallahi Gwamna shine baya da gaskiya. Dr. Abubakar A. Fari, jami’in da uwar jam’iyya ta kasa ta tura domin ya jagoranci zaben fidda gwani a jahar Zamfara, shine mai gaskiya, kuma wallahi, wannan mutum irin su muke bukata a kasar nan in dai har da gaske ne muna so mu gyara kasar nan.

Hakikanin abun da ya faru shine. Kuma idan nayi karya, Allah ya kama ni, idan na goyi bayan wani daga cikin ‘yan takarar nan, Allah ya hukunta ni da irin hukuncin da ya dace dani. Idan nayi ma wani sharri ko kazafi, sai ya kaini kotu, ko kuma Allah yayi masa sakayya. Dukkanin ‘yan takarar nan su tara, masu neman samun tikitin tsaya wa takarar Gwamna a jam’iyyar APC, a jahar Zamfara wallahi babu wanda ya sanni, ko ya taba ganina. Domin ni bama su ba, babu wani Dan siyasa da zai ce ina zuwa wurin shi neman wani abu. Alhamdulillahi, Allah ya kare ni daga wannan, kuma na gode masa akan haka.

Kawai ni bukata ta shine, in bayyana wa duniya gaskiyar abinda ke faruwa a jaha ta ta Zamfara, domin kubutar da jahar daga rudani da tashin hankalin siyasa da ake neman jefa ta, ba don komai ba, sai don son zuciyar wasu ‘yan tsirarun mutane. Saboda abun da na gani da ido na ya bani tsoro, ya tayar mani da hankali kuma ya gigita ni.

Yau sati daya kenan ina cikin garin Gusau a jahar Zamfara, tun ranar Asabar da ta gaba ta. Kamar yadda kowa ya sani ni Dan Gusau ne, Dan gida ba bako ba.

Tun rana ta farko da hedikwatar jam’iyya ta kasa ta tura wannan bawan Allan Dr. Abubakar A. Fari jahar Zamfara domin yin zaben fidda gwani, Gwamna yace shi bai yarda da shi ba. Meye laifin sa a wurin Gwamna? Laifin sa shine: Domin yace gaskiya za’ayi, domin yaki karbar cin hancin su, domin yaki yarda su saye shi ya zalunci Zamfarawa, domin yaki yarda ma ya tafi wurin su su bashi masauki, sai ya wuce kai tsaye wurin kwamishinan ‘yan sanda. Duk yadda Gwamna zai yi a juya mutumin nan ya zubar da mutuncin sa ya karbi wani abu ayi yadda ake so, bawan Allan nan wallahi yaki yarda. Tsakani na da Allah, wannan shine laifin wannan mutum a wurin Gwamna.

Kuma wannan mutum Dr. Abubakar A. Fari, wallahi ya haihu, kuma ya kai da. Don haka, ya kamata ma mai girma Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sani, irin wadannan mutane sune ainihin abokan aikin sa, da zasu taimaka masa wurin yakar cin hanci da rashawa, ire-iren su ne zasu taimaka masa wurin gyara Nigeria. Domin wannan mutum, wallahi mutum ne mai gaskiya, mai rikon amanah, wanda ba duniya ce a gaban sa ba.

Bangaren Gwamna sun nemi ya basu dukkanin hadin kai domin a danne sauran ‘yan takarar, amma mutumin nan ya kafe, yaki yarda, yace shi gaskiya kawai za’a yi wurin zaben nan.

Laifin shi na farko shine, yaki yarda ya sauka a wurin su su bashi masauki, daga nan su samu damar tattaunawa da shi. Na biyu yaki karbar cin hanci ayi zalunci. Na uku shine sun tura ‘yan ta’addar su wurin zabe, suka kori mutane da duka da sara, da cin mutunci iri-iri, suka yi abinda suke so na son zuciya zalunci, shi kuma ya soke zaben yace sam bai yarda da shi ba. Wallahi kar ka kara kar ka rage, wannan shine laifin wannan jami’i a wurin su. Don haka suke ta kumfar baki su basu yarda da shi ba.

Duk wanda yake cikin jahar Zamfara yasan abun da ya faru ranar laraba da aka yi zaben nan. Gwamnati ta tura ‘yan ta’adda suka afka wa mutane da duka da sara da harbi. Sun ci mutuncin mutane, har da matan aure da tsofaffi da suka fita domin gudanar da wannan zabe.

Wasu sun karye, wasu sun yi rauni mai tsanani, yawanci mutane sun koma gida jina-jina, kai har da rasa rayuka, domin a wannan ranar mutum tara aka kashe a jahar Zamfara, domin kawai gwamnati tana so ta kakaba wa mutane Dan takarar da basu so da karfi da yaji, su kuma mutanen jaha sun ce sam basu yarda ba, sai dai a bar su su zabi wanda suke so.

Gwamnati ta raba kudi da kayan masarufi, domin dai jama’ah su mika wuya, su yarda da Dan takarar da ta kawo, amma duk da haka jama’ah sun ki yarda. Na san wanda ya raba kudin runfuna, nasan wadanda suka raba wa matasa ‘yan ta’adda dari biyar-biyar suka yi abinda suke so, duk abinda ya faru a idon mu aka yi shi.

An watsa ma mata, tsofaffi, da sauran jama’ah tiya-gas domin dai duk a cimma nasarar zalunci, amma duk da haka jama’ar Zamfara dai sun kafe, sun ki yarda.

Don haka ya kamata duniya ta san halin da ake ciki a jahar Zamfara. Duk babatun da Gwamna yake yi a kafar yada labarai wallahi ba gaskiya bane. Sam basu da gaskiya. Suna so ne su kakaba wa mutane Dan takarar da jama’ah basu so da karfi da yaji.

Don haka mutane su sani, uwar jam’iyya, karkashin jagorancin Adams Aliyu Oshiomhole, sune masu gaskiya. Domin su kawai sun ce ne a tsaya tsakani da Allah ayi abunda jama’ah suke so. Shi kuwa Gwamna yace sam ba haka ba, sai dai a bar su suyi son zuciyar da suka ga dama.

Ta yaya za’ayi Gwamna da mukarrabansa duk inda suka shiga cikin jahar Zamfara ake yi masu ihu, ake jifar su, in har suna da gaskiya, kuma jama’ah suna son su? Ni fa wallahi ganau ne ba jiyau ba. Duk abinda ke faruwa a idon mu yake faruwa. Duk inda Gwamna ya shiga, ko wani jami’in gwamnati a Zamfara, wallahi jifar su ake yi ana yi masu ihu. Me ya kawo haka? Saboda Zamfarawa sun ce ba’a taba gwamnatin da suka sha wahalar ta, ta zalunce su kamar wannan ba. Don haka basu son Gwamna da duk wani Dan takara da zai kawo masu.

Wannan abun da nike fada wallahi shine gaskiyar lamari. Kuma ina fadar sa ne tsakanina da Allah, ba tare da shakkar wani mutum ko tsoron sa ba. Allah ne kawai a gaba na.

Kuma ni ban san dalilin da yasa kafafen yada labarai ba zasu ji tsoron Allah su ruwaito ma al’ummah ainihin gaskiyar abinda yake faruwa a jahar Zamfara ba?

Daga karshe ina mai cewa, jama’ah su sani: DAGA CIKIN WADANDA BA’A KARBAR SALLARSU AKWAI:

“Limamin da ya jagoranci Sallah, alhali mutane ba sa son limancinsa.” [Imamu Tirmizi ne ya ruwaito kuma ya inganta shi]

Wannan a limancin Sallah kenan fa, TO INA GA JAGORANTAR AL’UMMAR JIHA KO KASA BAKI DAYA!!!

Don haka Musulunci addini ne mai kimantawa da darajjanta zabin mutane, don haka shuwagabanni da masu ruwa da tsaki a zabe, su ji tsoron Allah, su zabawa al’umma shuwagabannin da suke da ra’ayi da su, kuma suke son su. Idan ba haka ba kuwa, zaman lafiya zai yi wuya a cikin al’ummah. Allah ya sawwake kuma Allah yasa mu dace, amin.

Dan uwanku:

Imam Murtadha Muhammad Gusau. Za’a iya tuntubar sa a wannan adireshi kamar haka: gusaumurtada@gmail.com ko kuma +2348038289761.

Tags: APCBuhariGusauHausaLabaraiNajeriyaPREMIUM TIMESYarizabeZamfara
Previous Post

TATTAUNAWA: Ni ne dan takarar PDP da zai iya kada Buhari a zaben 2019 – Kwankwaso

Next Post

Yamutsin Kujerar Sanatan Kaduna ta Tsakiya: Shehu Sani ne dan takarar jam’iyyar APC – Uwar Jam’iyya

Next Post
Sani shehu

Yamutsin Kujerar Sanatan Kaduna ta Tsakiya: Shehu Sani ne dan takarar jam'iyyar APC - Uwar Jam'iyya

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • ƘURUNƘUS: Atiku Abubakar ya lashe zaɓen fidda ɗan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar PDP
  • ZAƁEN FIDDA-GWANI: Cin hancin da ‘deliget’ za su karɓa a hannun ‘yan takara zai ƙasa dagula matsalolin da ƙasar nan ke fama da su -Sheikh Gumi
  • FIDDA-GWANIN PDP 2023: Tambuwal ya janye ya ce ya na bayan Atiku
  • IDO NA GANIN IDO: Dalilin baza jami’an mu filin zaɓen fidda-gwanin PDP a Abuja -EFCC
  • TURA TA KAI BANGO: Dalilin da ya sa dole na hakura da takarar sanatan Kebbi – Aliero

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.