• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Nigerian Pilgrims

    HAJJIN BANA: Duk wanda ya zarce shekaru 65 bashi ba Hajji bana – Hukumar Alhazai

    Beggars

    Almajirai da mabarata sun kwararo Abuja – Mahukunta

    HARƘALLAR KWANGILA: EFCC ta kama Patricia Etteh, tsohuwar Kakakin Majalisar Tarayya

    HARƘALLAR KWANGILA: EFCC ta kama Patricia Etteh, tsohuwar Kakakin Majalisar Tarayya

    Ƴan bindiga sun ƙona hedikwatar karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra

    Ƴan bindiga sun ƙona hedikwatar karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Ba ni da ra’ayin takarar shugaban kasa, lokacin da aka zabe ni gwamnan Kaduna gashin kai na baki wul yanzu duk furfura – El-Rufai

    KALAMAN ƁATANCI GA ANNABI: Duk wanda ya yi zanga-zangar addini a Kaduna zai ɗanɗana kuɗar sa – Gargaɗin El-Rufa’i

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Nigerian Pilgrims

    HAJJIN BANA: Duk wanda ya zarce shekaru 65 bashi ba Hajji bana – Hukumar Alhazai

    Beggars

    Almajirai da mabarata sun kwararo Abuja – Mahukunta

    HARƘALLAR KWANGILA: EFCC ta kama Patricia Etteh, tsohuwar Kakakin Majalisar Tarayya

    HARƘALLAR KWANGILA: EFCC ta kama Patricia Etteh, tsohuwar Kakakin Majalisar Tarayya

    Ƴan bindiga sun ƙona hedikwatar karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra

    Ƴan bindiga sun ƙona hedikwatar karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Ba ni da ra’ayin takarar shugaban kasa, lokacin da aka zabe ni gwamnan Kaduna gashin kai na baki wul yanzu duk furfura – El-Rufai

    KALAMAN ƁATANCI GA ANNABI: Duk wanda ya yi zanga-zangar addini a Kaduna zai ɗanɗana kuɗar sa – Gargaɗin El-Rufa’i

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

ZANCE NA GASKIYA: Cutar Sankarau, Daga Bello Muhammad

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
April 15, 2017
in Rahotanni
0
ZANCE NA GASKIYA: Cutar Sankarau, Daga Bello Muhammad

Tun muna yara ‘yan kanana mun san ana cutar sankarau. A wancan lokacin mun san ita wannan cuta ta sankarau, ba a lokacin damina ko sanyi ake samunta ba, tana zuwa ne a lokacin da ake tsananin zafi.

Haka kuma mun sani a bisa al’ada har zuwa yau yara kanana a wannan nahiya tamu ba a yi musu kaciya sai a lokacin sanyi. Malaman kimiyya na gargarjiya, wato wanzamai, su sun haqqaqe kaciya ta fi saurin warkewa idan an yi ta a lokacin sanyi.

Har wala yau, cutar kurkunu, wanda na daina jin labarinta kwata-kwata tafi yaduwa da yawa a lokacin damina. Sauro ma yafi kara-kaina a lokacin zafi da damina, cutar da yake yaxawa ta maleriya ta fi kamari a zafi da damina.
Duk wadannan batutuwa ilmi ne,kuma tabbatacce, babu wanda yake ja da wannan batu a tsawon lokaci. Ilmi ne wanda kunne ya girmi kaka.

Masu bin kafafen labarai sun ji cewa zuwa jiya Litinin ministan harkokin lafiya na kasa Farfesa Onyebuchi Ezekeil, ya bada bayani cewa an samu vullar cutar sankarau a jihohi 19 na Najeriya, a sakamakon vullar cutar har an rasa rayuka sama da 400, sannan ga mutum dubu hudu suna cikin halin damuwa mai ban tsoro a duk fadin kasar dangane da wannan cuta ta sankarau. Ya fadi wannan bayani ne a Gusau, jihar Zamfara inda akalla yara 230 suka rasa rayukansu sakamakon wannan musiba.

A yau kuma a jihar Kaduna, ministan ya yi bayanin cewa gwamnati ba ta da wani shiri akan wannan sabuwar Sanqarau TYPE C, ita shirin da take da shi shi ne akan abin da aka saba gani na cutar da ake yi wa laqabi da Sanqarau TYPE A.

Abin da ya fi daukar hankali tun bayan bullar wannan annoba da suka saba ji da gani shi ne sabuwar fassarar abin da ya jawo cutar.Tun fil azal, masana sun nuna zafi da cunkoso da rashin iska sune suke qarawa wannan zazzabi kwarin gwiwa idan kwayar sa ta bakateriya ta fara yaduwa. Da wahala kuma a danginku a ce an rasa wanda wannan cuta ta tava kashewa a shekaru 100 da suka gabata tun lokacin da aka fara jin duriyarta.

Ma’aikatar lafiya ta qasa da haxin gwiwar takwarorinta na jihohi sukan yi tanadi akanta idan zafi ya fara nuna alamun shiga.Musamman kuma a bana, masana sun bada gargadi cewa za a samu sanqarau mai muni kuma TYPE C, don haka a yi maza-maza a xauki matakan rigakafi.

Amma kuma kwatsam sai ga gwamnan jihar Zamfara yana shaida wa duniya cewa wannan cuta ta sankarau abin da ya kawo ta ba abin da mutane suka saba ji bane ko wanda suka sani na asali, wannan karon sabon Allah ne da ya yi yawa, musamman kuma zinace-zinace shi ne dalilin da ya sanya Allah ya kawo cutar da tafi kowa qarfi ta faskari duk wani magani ta ke kashe mutane cikin qiftawa da bisimilla.

A fahimtar Alhaji Abdul Aziz Yari, wanda kuma shi ne shugaban kungiyar gwamnoni ta qasa wato Nigerian Governors Forum mutane su koma ga Allah su gyara tsakaninsu da shi, sai a warware daga wannan tashin hankali da musiba.

Ba shakka Allah SWT yana jarrabtar bayinsa da musibu iri-iri domin su hankalta sannan kuma su koma gare shi.

Amma irina za su gamsu da fahimtar Abdulaziz Yari ne kawai idan da gwamnatinsa ta jihar Zamfara ta yi tanadi bisa shawarwarin masana domin dakile wannan musibar da an gaya musu tana zuwa.Sun yi bakin kokarinsu, sai ta gallabesu, sai mu ce eh yana da hujja. Amma ya zauna yana ta yawo, yana sharholiyarsa, bai zama a Gusau, bai zama a Talatar Mafara, cuta ta vulla, kawai sai a ce Allah ne? Allah ai baa bin wasa bane! Ai ita musibar da Allah ya ke aikowa tana zuwa ne ga muatne ba shiri wato bagatatan. Amma Sankarau ai an san shi da gidansu, da unguwarsa da iyayensa, kuma an saba da shi, har na bana wannan sabon akwai labarin zai zo.

Zan kuma iya yarda da matsayin AbdulAziz Yari da a ce wadanda cutar ta ke kashewa ba yara bane. Akasarin mutanen jihar Zamfara 230 da suka rasa rayukansu a wannan annoba, ‘yan yara ne qanana da suke qasa da shekara goma. Masu wannan shekaru a shari’ar Musulunci basa xaukar laifi kama Allah ba zai kama su ba, suna can makarantar Annabi Ibrahim AS. Idan muka yarda da matsayin gwamna Yari, mun gamsu kenan Allah (SWT) mai sabawa ne ciki maganganunsa kuma yana hukunta wanda laifi bai shafe shi ba. Ba kuwa haka bane.

A hankalce kuma in aka dogara ga fahimtar AbdulAziz Yari, duk wani magani da za a nema daga WHO ko UNICEF ko qasashen Turai da Larabawa da Asiya bai dace ba, tunda cutar ta fi qarfin tunanin xan adam, zura ido za a yi a ci gaba da addu’a kuma ana yakar alfashar zina, sai Allah ya kawo sauqi. Wannan kuwa mustahilli ne.

A zance na gaskiya abubuwa biyu ne ko uku za a yi domin shawo kan wannan matsala a yau da guje mata a gobe. Na farko mu daga hannu mu roki Allah mu nemi taimakonsa domin ya kawo mana sauqi da rangwame a cikin irin wannan halin da muka shiga na wannan annoba. Na biyu kuma mu fita neman magani a ko ina yake a duniya domin tseratar da rayuwar al’ummarmu, yana daga cikin alqawura da rantsuwa da shugabanni suke karva idan sun hau mulki na tsare dukiya da rai da lafiya.Wajibi ne gwamnoni da shugaban qasa da duk masu alhaki a cikin wannan sha’ani su bi duk wata hanya da duk wata dabara domin a kau da ita. Rai fa na mutum xaya ba abin wasa ba ne. Na karshe kuma shi ne , duk abin da yake rataye a wuyan gwamnati, kuma ta san alhakinta ne, ya zama tilas ta riqa daukar mataki a kan lokaci tun kafin ya zo ya gagara warwarewa. Sankarau din nan an san shi kuma ana da labarin cewa yana nan tafe da sabon salo mai muni, ba daidai bane a yi sakaci, sai ya zo kuma a dorawa Allah mahalicci laifi, har ma a yi masa karya.

Irin wannan fahimta da Yari yake son mutane su hau kanta su zauna, ba zata taimaka mana ba a samu shawo kan wannan mas’ala ta didindin. Ai wasu kasashe da yawa a duniyarmu ta yau inda suke da zafi sun yi bankwana da cutar Sankarau, kai idan muka yi la’akari da tarihin Sanjarau a Najeriya, za mu ga cewa akasarin jihohin da abin ya fi shafa suna yankin Arewa, ko a wannan zafin jihohin kudu hudu ne abin ya shafa, sauran 15 a Arewa ne. Ka ga za a iya maganinta in an ga dama.

Za a iya samun Bello Muhammad Sharada a:bellosharada@gmail.com

Tags: HausaKanoLabaraiNajeriyaNewsPREMIUM TIMESSankarau
Previous Post

Dr Bilal Philips ya ziyarci jihar Bauchi

Next Post

Me Ya Dabaibaye EFCC? Daga Ashafa Murnai

Next Post
Me Ya Dabaibaye EFCC?  Daga Ashafa Murnai

Me Ya Dabaibaye EFCC? Daga Ashafa Murnai

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • HAJJIN BANA: Duk wanda ya zarce shekaru 65 bashi ba Hajji bana – Hukumar Alhazai
  • ZANGA-ZANGAR MATAN AURE: Ƴan mata na kwace mana mazaje da irin matsatssun kayan da suke saka wa
  • Almajirai da mabarata sun kwararo Abuja – Mahukunta
  • ZARGIN YUNƘURIN KOMAWA APC: Sule Lamiɗo ya ce El-Rufai tantirin maƙaryaci ne
  • HARƘALLAR KWANGILA: EFCC ta kama Patricia Etteh, tsohuwar Kakakin Majalisar Tarayya

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.