Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa za ta gina gidaje dubu ɗaya a jihohi bakwai na Arewacin Najeriya.
Jihohin bakwai da za a gina gidajen sun haɗa da Sokoto z Kebbi, Katsina, Zamfara, Kaduna, Neja da Benuwai.
Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ne ya bayyana haka, tare da cewa shirin gina gidajen na daga wani ɓangare na tsare-tsaren magance matsalolin rikice-rikicen da ke faruwa a Arewa.
Shettima ya bayyana a lokacin da ya wakilci Shugaba Bola Tinubu ranar Juma’a, a Maiduguri, wurin ƙaddamar da ayyukan raya ƙasa da Gwamna Umara Zulum ya yi a kwanaki 100 ɗin farko na zangon sa na biyu.
Shettima ya ƙara da cewa Gwamnatin Tarayya ta amince za ta ware Naira biliyan 50 domin domin ta bai wa Hukumar Agajin Gaggawa, NEMA domin fara shirye-shiryen tsarin ‘Pulaku’ a Arewa, wanda za a fara domin shawo kan rikice-rikicen makiyaya da manoma a Arewa maso Yamma.
“Shugaban Ƙasa ya amince a gina gidaje 1,000 a jihohin Sokoto, Kebbi, Katsina, Zamfara, Kaduna, Neja da Benuwai.
“Gidajen kuma za a gina masu makarantu, asibitoci, asibitocin dabbobi, wuraren kiwo ga Fulani makiyaya. Kuma ya ce A Kaduna da Benuwai duk wanda rikicin ya shafa sai an tallabe shi.”
Shettima ya ƙara da cewa kowane ɓangaren ƙasar nan zai ci moriyar Gwamnantin Tinubu.
Ya ce kuma Gwamnatin Tarayya za ta sake farfaɗo da shirin noman alkama a faɗin ƙasar nan.
Ya ce Shugaban Ƙasa Bola Tinubu na sane da dukkan ƙalubalen da ke damun Najeriya, kuma a shirye ya ke ya magance su.
Discussion about this post