Shugaban jaridar THISDAY da Arise TV Channel, Nduka Obaigbena, ya ƙalubalanci daraktocin yaɗa labaran kamfen ɗin Bola Tinubu cewa su gabatar da shi a Arise TV domin a yi masa tambayoyin gar-da-gar.
Obaigbena ya yi wannan ƙalubale ga Dele Alake da kuma Bayo Onanuga cewa ‘yan Najeriya na da tafka mahawara da Tinubu, domin su san makamar shugabancin sa idan ya yi nasara a zaɓen 2023.
Obaigbena ya yi wannan ƙalubale a ranar Laraba, a matsayin martanin da Alake da Onanuga su ka sha yi cewa Obaigbena da Arise TV ba su ƙaunar TInubu, kuma sun shirya masa wata ƙullalliya ce idan ya amsa gayyatar taron ganawa da shi da Arise TV da THISDAY.
A gefe ɗaya kuma ‘yan Najeriya da ‘yan adawa sun damu da yadda Tinubu ya sha kauce wa taron ganawa da shi, har sau huɗu, amma sai ya tafi Landan inda ya yi hira da jaridun Turai.
A nata ɓangaren rundunar yaƙin neman zaɓen Tinubu ta na zargin Arise TV da nuna son rai da adawa da TInubu.
Ko kwanan nan sai da rundunar yaƙin neman zaɓen Tinubu ta yi kira ga magoya bayan ta cewa su ƙaurace wa Arise TV.
Ranar Litinin ne Editocin THISDAY da Arise TV su ka fitar da sanarwar cewa Alake da Onanuga sun nemi a kori Rufai Oseni da Editan THISDAY, Shaka Momodu, a matsayin sharuɗɗan sasantawa.
Sai dai kuma rundunar yaƙin neman zaɓen Tinubu ita ma ta fitar da sanarwa a yammacin ranar Litinin ɗin cewa ƙarya Editocin THISDAY da Arise TV ke yi.
A nasa ɓangaren, Obaigbena ya ƙaryata zargin goyon bayan soke zaɓen 12 Ga Yuni, harƙalla a Ingila da Afrika ta Kudu, hannu a salwantar da dala biliyan 2.1 da ake zargin Sambo Dasuƙi ya yi.
Discussion about this post