Hukumar kiwon Lafiya ta Duniya ta bayyana cewa duk da cewa wasu kasashen duniya na fidda wasu magunguna na rigakafin cutar Korona, za a kai tsakiyar shekarar 2021 kafin a samu wanda aka tabbatar da ingancin sa.
Mai magana da yawun hukumar Margaret Harris, ta bayyana cewa hukumar bata amince da ingancin wadannan magunguna ba tukunna dukkan su sunananan a matakin gwaji.
Sai dai kuma tuni har kasar Rasha ta ce ta gama hada maganin rigakafin cutar har kuma ma ta fara amfani dashi.
Najeriya ta karbi samfurin wannan magani na rigakafi.
Ministan Kiwon Lafiya, Osagie Ehinare ya bayyana cewa an aika da wannan magani ma’aikatar NAFDAC domin cigaba da aiki a kai.
Discussion about this post