Karamin Ministan Kwadago Festus Keyamo, ya bayyana dalla-dallar irin ayyukan da matasa 774,000 da Shugaba Muhammadu Buhari ya sanar cewa tuni an fara shirin daukar su aiki a dukkan kananan hukumomin kasar nan.
Da ya ke ganawa da manema labarai kwanan baya, Keyamo cewa ya yi sai ranar 1 Ga Oktoba matasan za su fara aiki.
Sannan kuma ya ce a ranar, za a fara ne da gwaji a jihohi takwas tukunna.
Jihohin da Kiyamo ya ce za a fara aikin sun hada da Adamawa, Barno, Ekiti, Ebonyi, Edo, Jigawa, Kwara da kuma Katsina.
Minista Keyamo ya ce za a fara ne da matasa 40,000 a wadannan jihohi takwas, kafin daga nan kuma a ci gaba a sauran jihohin kasar nan.
Irin Ayyukan Da Za Su Rika Yi A Kan Naira 20,000 A Wata:
Keyamo ya ce ayyuakan na su akasari duk ci-da-karfin-ka ne da suka hada da:
1. Yin amfani da diga da cebur da minjagara su na ginin kwalbatoci, ginar ramu da kuma aikin fitikin sare ciyawar da ke gefen titi.
2. Sassabe, shara da kaftun hanyar ruwan da ke kwarara daga madatsar-ruwa zuwa cikin cikin gonakin noman rani.
3. Aikin ginin hanyoyin shararra da burji da gyaran hanyoyin.
4. Rainon sabbin shuke-shuken itatuwa da yi musu ban-ruwa a jihohin Jigawa, Barno da Katsina.
5. Kula da warware matsalar cinkoson ababen hawa a kan titina.
6. Shara da goge-goge a makarantu, asibitoci da wasu ofissoshin gwamnati.
Premium Times Hausa ta buga labarin albishir din da Buhari ya yi a Ranar Dimokradiyya cewa gwamnatin sa ta fara Shirin Samar Da Ayyukan Musamman ga
matasa 774,000, don yaye musu talaucin Coronavirus.
Shugaba Muhammadu Buhari ya ce Gwamnatin sa ta fara wani gagarimin shiri na gaggauwar daukar matasa 774,000 aiki na musamman, domin yaye musu kuncin rayuwar da jama’a suka shiga sanadiyyar barkewar cutar Coronavirus.
Da ya ke jawabi a ranar Juma’a yayin tunawa da Ranar Dimokradiyya, wadda ta koma 12 Ga Yuni, Buhari ya ce cutar Coronavirus ba karamar illa ta yi wa milyoyin jama’a ba.
“Da yawa sun rasa iyalai, ‘yan uwa da masoyan su. Wasu sun rasa aikin su baki daya. Milyoyi sun rasa dukiyoyin su. Tattalin arzikin wasu ya karye dalilin cutar Coronavirus.”
A kan haka ne Buhari ya ce gwannatin sa ta raba kayan tallafin rage radadin talauci da kuma raba bilyoyin kudade ga milyoyin marasa galihu a kasar nan.
Da ya juya a kan ayyukan musamman da ya ce gwamnatin sa za ta samar wa matasa kwanan nan, Buhari ya ce za a tsamo matasa 1,000 ne daga kowace karamar hukuma daga Kananan Hukumomi 774 da ake da su a fadin kasar nan.
Ya bada hakuri dangane da irin matsanancin halin kuncin da ‘yan Najeriya suka shiga, dalilin tsauraran matakan da gwamnatin tarayya ta dauka domin kokarin dakile cutar Coronavirus.
Ya ce cutar abin tsoro ce ganin yadda ta fara kamar da wasa a kasar China, amma ga shi cikin ‘yan watanni ta shafi mugum sama da milyan 7 a duniya a cikin kasashe 216.
Ya ce jo shakka babu Coronavirus babbar barazana ce ga rayuwar dan Adam gaba daya a duniya da kuma tattalin arzikin duniyar baki daya.
Idan ba a manta ba, Buhari ya rasa Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Abba Kyari sanadiyyar cutar Coronavirus da ya dauko a kasar Jamus.
Kyari dai an yi ittifakin cewa a gwamnatance, shi ne mutumin da ya fi kowa kusanci da Buhari, kafin Coronavirus ta yi sanadiyyar ajalin sa.
Discussion about this post