• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    SABODA TIWITA: Sanatocin PDP sun fice daga Zauren Majalisar Dattawa

    Zaɓaɓɓun Sanatocin Arewa ta Tsakiya sun nemi a ba su Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Ko a-yi-ta-ta-ƙare

    KIDAYA: An kashe naira biliyan 200 wurin shirye-shiryen fara ƙidayar jama’a – Shugaban Ƙidaya

    KIDAYA: An kashe naira biliyan 200 wurin shirye-shiryen fara ƙidayar jama’a – Shugaban Ƙidaya

    INEC ta rantsar da Isah matsayin kwamishina a karo na biyu

    INEC ta rantsar da Isah matsayin kwamishina a karo na biyu

    ƘAƘUDUBAR TALLAFIN FETUR: Buhari ya bukaci majalisar Dattawa ta amince masa ya tattago bashin dala miliyan 800

    AYYUKAN BAN-KWANA DA GWAMNATI: Buhari ya damƙa filin jirgin Kano da na Abuja ga Amurkawa

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    SABODA TIWITA: Sanatocin PDP sun fice daga Zauren Majalisar Dattawa

    Zaɓaɓɓun Sanatocin Arewa ta Tsakiya sun nemi a ba su Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Ko a-yi-ta-ta-ƙare

    KIDAYA: An kashe naira biliyan 200 wurin shirye-shiryen fara ƙidayar jama’a – Shugaban Ƙidaya

    KIDAYA: An kashe naira biliyan 200 wurin shirye-shiryen fara ƙidayar jama’a – Shugaban Ƙidaya

    INEC ta rantsar da Isah matsayin kwamishina a karo na biyu

    INEC ta rantsar da Isah matsayin kwamishina a karo na biyu

    ƘAƘUDUBAR TALLAFIN FETUR: Buhari ya bukaci majalisar Dattawa ta amince masa ya tattago bashin dala miliyan 800

    AYYUKAN BAN-KWANA DA GWAMNATI: Buhari ya damƙa filin jirgin Kano da na Abuja ga Amurkawa

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

KORONA BAROS: Tsumagiyar Kan Hanya, Daga Dr Nuruddeen Muhammad

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
April 1, 2020
in Labarai
0
Blood sample with respiratory coronavirus positive

Blood sample with respiratory coronavirus positive

Bayan na kammala duba marasa lafiya a wani yammaci, ban san lokacin da na tsinci kai na cikin tunanin irin sa’ar da na yi kasancewata cikin ƙoshin lafiya ba. A wani gefe kuwa na shiga yanayin tausayawa ga waɗanda Allah SWT ya ɗorawa larurar rashin lafiya. Babu abun tausayi a duniya kamar maras lafiyar da bai da d’an abun hannunsa da zai nemi magani, karma a ce rashin lafiyar ta kasance ta ko a mutuce ko a yi rai. Amma mu likitoci kan ci karo da ire-iren waɗannan matsaloli a kullum, musamman ma a asibitocin gwamnati. A takaice dai, babu fa wata sana’a da za ta sa mutum ya ga tsananin talauci da kuma sheda raɗaɗinsa kamar zama Likita a Najeriya. A asibitocinmune za ka ga bil’adama ya juya bayansa yayi tafiyarsa gida da tabbacin cewa mutuwa zai yi saboda kawai bai da Naira dubu ashirin (20,000) ko dalilinta! Haka dai Malam talaka a wannan ƙasa ke mutuwarsa ke kukansa shi kaɗai. Amma fa a inda gizo ya ke saƙar shine, idan dai ba wata kiyayewar Allah SWT ta musamman ba, toh fa su kan su shafaffu da man na daf da ɗanɗana kuɗarsu!

Cutur numfashi ta korona baros ta sako ɗan Adam a gaba. Annobar ta zama gagara badau, gobara daga kogi maganinki sai Lillahi, duba da yadda ta fara lallasa ƙasashen da suka fi kowaɗanne ƙarfi a duniya. Cutar, ta yi ɗiban karan mahaukaciya da ƙasashen da su ka yi fice a ƙarfin tattalin arziki, da ƙarfin makaman ƙare dangi, da ƙarfin tsarin kiwon lafiya, da kuma lafiyayyun al’umma. Korona baros dai ta zama tsumagiyar kan hanya, ki shafɗi babba ki shafɗi yaro, wadda ba ta ware bambamcin launin fata, ko ƙarfin arziki, ko kuma aƙida.

Ƙasashen yammacin turai da arewacin Amurka, da kuma ma su arziki na nahiyar Asiya sun kere sa’a wajen kula da mutanensu da kuma son more rayuwa. Sun ɗaukaki rayuwar duniya ta yadda babu abinda suke tsoro kamar barinta. Hakan ya sa suka tsunduma cikin duniyar kimiyya har ta kai da cewa ku san ba abun da ba su samo maganinsa ba sai dai mutuwar ita kan ta. Sun sa tsufa a gaba sai da suka rage masa gudu. Sun yi kutse cikin taswirar halittar ɗan adam (wato DNA) domin ƙera wasu daga cikin sassan jiki. Sun kuma yi tanade-tanade irin na gayawa jini na wuce domin yanayin rashin lafiya na gaggawa. Kyakkyawan misali shine; a yau a birnin New York na Amurka an kai matakin da duk wani kira na gaggawa daga ɗan ƙasa da bai samu ɗauki cikin kimanin mintuna tara da rabi ba to tilas hukomomi sai sun bi ba’asi sun kuma ɗauki mataki na ba sani ba sabo.

Amma mu anan Najeriya za a iya cewa rashin sani (wadda ake cewa ya fi dare duhu) a tsakankanin shafaffu da man mu ya sa su tunanin cewa za su iya yin baba na ɗaka gemu na waje. Bi ma’ana, su a na su ɗan ƙaramin tunanin, za su iya son ran su yadda su ke so anan gida Najeriya, amma kuma su tsallaka Turai domin su mori waɗancan tanade tanade na lafiya ma su inganci da su turawa su ka tsarawa ta su al’ummar. Ma su hannu da shuni dai sun mai da zuwa waje domin duba lafiyarsu ya zama jiki. A matsayinka na jami’in kiwon lafiya a ƙasarnan kuwa, dole watarana sai ka haɗu da wanda zai yaɓa ma ka irin wannan batu a fuskarka. Akwai yanayin raini da wannan mutane ke da shi; mai kamar cewa ni fa waɗannan asibitocin na ku ba irin nawa ba ne. Amma fa batun gaskiya anan shine: shin idan wani abu na gaggawa ya taso makwabta za’a naimo ko kuwa abokan hulɗa da ke can nesa? Da yawa harda waɗanda za su iya ɗaukar ɗawainiyar naiman lafiya a ko ina a faɗin duniya na mutuwa kullum a ƙasarnan ta silar bugawar zuciya da sauran makamantan cututtuka. Hakan na faruwane saboda ita dai bugawar zuciya ba ta jiran lokacin da ya wuce mintina talatin zuwa awa guda, ga shi kuma mu kwata kwata ba mu da wani tsari da k’warewa, da kuma isassun kayan aikin bada taimakon farko da kuma agajin gaggawa (emergency).

Babu wani abu da zai ƙara fallasa ainahin mummunan yanayin da harkar lafiyarmu ke ciki kamar wannan annoba ta Korona Baros. Ita dai wannan cuta idan tayi tsanani ta kan maƙure numfashin mutum ne, ta hanashi shan iska saboda lalata huhu da ta ke yi. A irin wannan yanayi kuwa kusan duk marasa lafiyar na buƙatar taimakon sinadarin iskar numfashi (wato oxygen). Wa su kuwa daga cikinsu har sai an kai ga ɗorasu akan injin numfashi na bentileto (ventilator).

Ita dai bentileto wata na’urar asibitice ta musamman mai taimakawa da numfashi wadda ke buƙatar likitoci na musamman (Anesthetics) domin sarrafa ta. Yau ƙasar Italiya ta shiga ƙarancin duka biyun, duk da kuwa cewa ƙasar na ɗaya daga cikin ƙasashe goma da su ka fi kowaɗanne ingancin tsarin kula da lafiyar al’ummarsu a duniya. Yanzu haka a arewacin ƙasar Italiyan, ƙwararrun likitocin da su kan su sun gajiya, ke yanke hukuncin wa zai rayu wa kuma zai mutu saboda ƙarancin na’urar bentileto.

Akwai dai darussa ma su dama da amafani ga Gwamnatoci da mu kammu ƴan Najeriya da ya kamata mu kiyaye daga wancan yanayi. Na farko dai dolene muɗauki dukkanin matakan kariya domin kare kawunanmu daga kamuwa da wannan cuta. Saboda da haka, abun a yabawa hukumomine, yadda mutanenmu da ke dawowa daga ƙasashen waje ke tabbatar da ingancin tsare-tsaren da aka tanadar a duk filayen tashi da saukar jiragen sama na Ƙasa da Ƙasa da mu ke da su a faɗin ƙasarnan. Amma fa akwai sauran aiki a gabanmu

Bijirewa gwaje-gwajen da aka tanadar a filayen jiragen da wasu mambobin majalisar tarayya su ke yi ba komai bane face nuna zallar rashin wayewa da ƙarancin sanin ya kamata a fili. Hakan misaline na irin tsantsar gadara da ƙafafa na wasu daga cikin shuwagabanninmu da ke kawo bala’in da kowama sai ta shafe shi. Shugaban ƙasa Muhammad Buhari yayi dai-dai da ya aikewa duka majalisun biyu da zungureriyar takarda dake gargaɗinsu akan waɗannan ɗabi’u.

Mu kuma ƴan Ƙasa a namu ɓangaren, dolene fa muzage dantse mu kiyaye dukkanin ƙa’idojin da masana da hukomomi su ke faɗa. Musamman ma na rage cinkoso, da yawaita wanke hannu, da kuma zama a cikin gida idan da damar yin hakan. Sannan kuma sai mu koma kan buzu domin yin addu’o’i da kuma tuba ga Ubangijinmu domin ya karemu daga wannan cuta, musamman ma irin nau’inta mai tsanani da kasashen Amurka da Italiya ke fama da shi.

Domin kuwa a duk faɗin Najeriya fa ba mu da wannan na’urar numfashi ta bentileto (ventilator) da ta wuce guda Ɗari Biyu kacal. Sannan su kan su ɗari biyun na tattarene a manyan manyan asibitocin da ke manyan birane irin su Lagos, Abuja, Ibadan, Kano, Zaria da Fatakwal. Idan ka ɗakko wannan matsalar sannan ka ƙarata akan matsalolin asibitocinmu na yau da kullum irin na rashin wadatattu da kuma ingantattun kayan aiki da gadajen kwantar da marasa lafiya, da kuma rashin ƙwararrun ma’aikata, za ka gane cewa idan fa wannan cuta ta sakomu a gaba (Allah ya kiyaye) kamar yadda ta saka waɗancan ma su jan kunnen, toh fa sai ɗan buzun mu! Bambamcin dai kawai shine, a wannan karon, yadda aka dama haka kowa zai sha. Domin kuwa waɗanda a da ke guduwa Turai domin neman lafiya yanzu babu gurin zuwa. Ai dama duk girman duniyarnan dai kowa ya san gidan ubansa; duk da kuwa ƙoƙarin cureta wuri guda da a ke ta faman yi. Zuwan Korona baros kuma ya ƙara tabbatar mana da cewa giji dai lahira ce, kuma na ka dai dole sai na ka!

Akwai ƙwararan darussa kuma marassa daɗi da za a samu bayan wannan iftil’ain ya wuce. Ala dole sai wannan gijin na mu mai suna Najeriya ya zauna ya nutsu ya kuma san inda kansa ke masa ciwo. Zuwan Covid 19 ya sa lafiya ta ƙara tabbatarwa da kowa a duniya cewa ita ce dai uwar jiki, wadda Mallam bahaushe ke cewa ‘sai da ke aka cin duniya, har ana ta marmari, har ana rawar jiki’. A saboda haka, ina da kusan tabbacin cewa duniya za ta zabura bayan wannan annobar. Za kuma ta shiga yin sabon shirin ko ta kwana – kamar yadda ta yi bayan barazanar nukiliya. Amma a wannan karon, za ta garzayane neman sabbin ilmin kiwon lafiya, da neman sani na musamman, da ƙirƙire – ƙirƙire da kuma uwa uba angiza magudan kuɗaɗe a gine ginen asibitoci da kayan aiki da horar da ƙwararru.

Mu ma dai a Najeriya dole mu shiga taitayinmu, mu kuma tsunduma a cikin wannan gudun yada kwarin wanin da za a yi domin tabbatar da cewa ba a ci gaba da barinmu a baya ba. Yanzu dai ya rage namu mu tattara hankalinmu a wuri guda, mu kuma farka, sannan musan ina muka dosa. Lokaci yayi da za muyi watsi da son zuciyoyinmu, mu haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen yaƙar ɗai-ɗaikun banbance-banbance irin na siyasa, da ɓangaranci, da ƙabilanci dake tsakaninmu. A taƙaice dai, ba za mu taɓa iya tunkarar irin wannan ƙalubalen da ke gabanmu ba har sai mun zamto tsintsiya maɗaurin ki guda. A cikin irin wannan yanayi, tunanin cewa idan jifa ya wuce kaina toh ya fad’a kan uban kowa fa babban kuskurene. Tunda dai jifa irinna Korona ya nuna cewa zai iya yin kwana ya dawo ya fasa kan uban kowa ma!

Amma da yardar Allah SWT za mu ga bayan Korona Baros. Sai dai ya zama wajibi mu ƙudiri niyyar yin juyin juya hali a tsarin tunaninmu da kuma a aikace domin inganta harkar kiwon lafiyarmu. Domin ita fa harkar lafiya (ba ma ta Korona ba kawai) tamkar wata tsumagiyar kan hanyace, ta shafɗi Mallam Talaka ta kuma juya ta shafɗi Attajiri.

Nuruddeen Muhammad tsohon Ministane a Ma’aikatar Harkokin K’asashen Waje ta Najeriya.

Tags: AbujaBarosHausaKan HanyakoronaLabaraiNajeriyaNewsPREMIUM TIMESTsumagiya
Previous Post

CORONAVIRUS: Akalla mutane 40,000 sun mutu a duniya

Next Post

Dalilin da ya sa Coronavirus ta fi kashe maza fiye da mata – Bincike

Premium Times Hausa

Premium Times Hausa

Next Post
NCDC-CoronaVirus

Dalilin da ya sa Coronavirus ta fi kashe maza fiye da mata - Bincike

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • TASHIN HANKALI A FILATO: Miyetti Allah sun yi kururuwar Jasawa na shirin kakkaɓe su ƙarƙaf, an kwashe masu shanu 25,000 cikin mako biyu
  • SUN CI TALIYAR ƘARSHE: Sanata Lawan ya damu ganin kashi 70 bisa 100 na ‘Yan Majalisa sun faɗi zaɓe
  • RIGIMAR SHUGABANCIN MAJALISA: ‘Ina goyon bayan Abbas, shi zan yi wa kamfen wurjanjan’ – Wike
  • RASHIN SANI: Yadda jami’an Kwastam suka bindige ɗan uwansu Jami’i a shingen bincike
  • WALLE-WALLE DA RAYUKAN ZAMFARAWA: Yadda ilmi ya taɓarɓare, talauci ya ƙara katutu, mace-macen ƙananan yara ya yi muni a mulkin Matawalle

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.