• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Za a sheka ruwan sama kamar da bakin kwarya cikin kwanaki uku masu zuwa a jihohi 18 a Najeriya – NiMet

    Za a sheka ruwan sama kamar da bakin kwarya cikin kwanaki uku masu zuwa a jihohi 18 a Najeriya – NiMet

    RANAR ‘YANCI: ‘Yan Najeriya mazauna Landan sun nemi a yi wa gwamnatin NNPP a Kano adalci

    RANAR ‘YANCI: ‘Yan Najeriya mazauna Landan sun nemi a yi wa gwamnatin NNPP a Kano adalci

    JAllI-JOGAR BELIN DIEZANI A KOTUN LANDAN: Kotu ta hana Diezani fita yawon dare, da rana ma an ce ta maƙala na’urar gane duk lungun da ta shiga

    JAllI-JOGAR BELIN DIEZANI A KOTUN LANDAN: Kotu ta hana Diezani fita yawon dare, da rana ma an ce ta maƙala na’urar gane duk lungun da ta shiga

    Ƴan sanda sun damke wasu abokai ƴan kungiyar matsafa dake tsafi da kawunan mutane a Ilori

    Yadda ƴan sanda suka kama Ibrahim da ya yi garkuwa da Fatima, ya ƙarɓi kuɗi kuma ya yashe ta a Zariya

    Kotu ta kori gwamna Sule na Nasarawa, ta ce PDP ce ta yi nasara a zaɓen gwamna

    Kotu ta kori gwamna Sule na Nasarawa, ta ce PDP ce ta yi nasara a zaɓen gwamna

    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Za a sheka ruwan sama kamar da bakin kwarya cikin kwanaki uku masu zuwa a jihohi 18 a Najeriya – NiMet

    Za a sheka ruwan sama kamar da bakin kwarya cikin kwanaki uku masu zuwa a jihohi 18 a Najeriya – NiMet

    RANAR ‘YANCI: ‘Yan Najeriya mazauna Landan sun nemi a yi wa gwamnatin NNPP a Kano adalci

    RANAR ‘YANCI: ‘Yan Najeriya mazauna Landan sun nemi a yi wa gwamnatin NNPP a Kano adalci

    JAllI-JOGAR BELIN DIEZANI A KOTUN LANDAN: Kotu ta hana Diezani fita yawon dare, da rana ma an ce ta maƙala na’urar gane duk lungun da ta shiga

    JAllI-JOGAR BELIN DIEZANI A KOTUN LANDAN: Kotu ta hana Diezani fita yawon dare, da rana ma an ce ta maƙala na’urar gane duk lungun da ta shiga

    Ƴan sanda sun damke wasu abokai ƴan kungiyar matsafa dake tsafi da kawunan mutane a Ilori

    Yadda ƴan sanda suka kama Ibrahim da ya yi garkuwa da Fatima, ya ƙarɓi kuɗi kuma ya yashe ta a Zariya

    Kotu ta kori gwamna Sule na Nasarawa, ta ce PDP ce ta yi nasara a zaɓen gwamna

    Kotu ta kori gwamna Sule na Nasarawa, ta ce PDP ce ta yi nasara a zaɓen gwamna

    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

BARCELONA: Ba cire Valverde, Wanda ya maye gurbin sa

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
January 14, 2020
in Wasanni
0
BARCELONA: Ba cire Valverde, Wanda ya maye gurbin sa

Barcelona New Coach

A ranar Talata ne tsohon kociyan Barcelona, Ernesto Valverde da aka sallama jiya Litinin ya yi bankwana da kulob din a cikin fara’a da annashuwa. Ko ba komai dai, ya jefar da kwallon mangwaro, ya huta da kuda.

Mamakin da duniyar kwallo ke yi kuma shi ne yadda Barcelona ta kori Valverde, maimakon ta dauko kwararren kociya, wanda duniya ta sani, kuma ya shahara, sai ta dauko Quique Setien, tsohon kociyan da Real Betis ta kora a kakar wasan La Liga da 2018/2019, bayan da Betis din ta kare kakar a matsayin ta 10.

Duk ba wannan ne abin mamakin ba, Stien dai bai taba cin kofi ko na auna ruwan madarar-sukudaye ba, duk kuwa da cewa ya yi tsawon shekara da shekaru ya na koyarwa a kungiyoyi daban-daban.

Barcelona ta shiga rudu ko rududu cikin makon da ya gabata, inda shugaban ta Josep Maria Bartomeu ya shiga neman sabon kociya, alhali kuma ba a kori ko sallami Valverde ba.

Rahotanni sun tabbatar da cewa sun tuntubi tsohon dan wasan ta, Xabi Harnendez da Ronald Koeman, amma duk sun noke, saboda gudun samun takun-saka da shugabannin kungiyar a karkashin shugabancin Martomeu.

Duk da haka sai da Valverde ya yi tirenin na ‘yan wasan Barcelona a jiya Litinin, duk kuwa da cewa daga rannan ya san da wahalar gaske ya sake horas da kungiyar har abada.

A karshe dai da Xabi da Koeman suka nuna rashin bukata, sai aka rubuta sunayen Quique Sutien, Gabriel Milito da Mauricio Pochettino domin a darje, a zabi daya daga cikin su.

An yi mamakin yadda Barcelona ta yi tunanin daukar Pochittino, tsohon kociyan Tottenham, mutumin da ya ce shi a duniya da ya yi kociyan Barcelona, har gara ya dauki fartanya, ya koma gona ya yi noma.

Setien, wanda shi aka dauka a matsayin sabon kociya, bai taba lashe kofi ko da na gasar wasan lido ba. Kulob din da ya horas a shekarar da ta gabata, na 10 ya zo a gasar La Liga.

QUIQUE SITIEN: Ina Kiwon Shanu Barcelona Ta Dauke Ni Kociyan Ta

A jawabin da ya yi yau Talata wurin karbar ragamar kulob din daga hannun Valverde, sabon kociya Sitien ya ce, “A jiya war-haka ina gona ta wurin kiwon shanu a kauyen mu. Yau kuma ga ni a yau kuma ni ne kociyan ‘yan wasan da suka fi kowane shahara da kwarewa a duniya.

“Ai ana yi min tayi, ko lokacin minti biyar ban bata ba, sai na ce na amince, na karba.”

Shi kan sa Sitien ya yi matukar mamakin yadda Barcelona ta dauke shi koyar da wasa a kungiyar ta, kungiyar da a yanzu haka ita ce ta farko a La Liga.

Valverde Ba Dan-goyo Ba Ne

Ba cire Valverde ne ya fi ba masu kallo da masu sharhin kwallon kafa mamaki ba, maye gurbin sa da Sitien shi ya fi bada mamaki ga kowa, har ma ga ‘yan wasan kungiyar.

An yi tunanin za a cire Valvade tun shekarar 2019, bayan da Liverpool ta yi wa kubob din cin-kaca a gasar Champions League, cin-wulakancin da Barcelona ba ta taba kwasar buhun-kunya kamar sa ba, a tarihin kafuwar kungiyar.

Harkallar Cinikin ’Yan Wasa

Shugabannin Barcelona sun samu kan su cikin kwatagwangwamar cinikin ’yan wasa, yayin da suka bi ta barauniyar hanya suka sayi Neymar lokacin shugabancin Sandro Rossell, wanda Bartomeu ya gada.

Daga baya kotu ta daure Sandro shekaru biyu, bayan samun sa da aka yi da laifin harkalla.

Shi ma Bartomeu sai da aka zarge shi da damfara, amma dai ya yi ta shige-da-fice ya na kokarin kare kan sa.

Da Asara Gara Gidadanci

Sandro da Bartomeu sun hada kai sun sayar da Neymar ga PSG fam milyan 222, wadanda suka kwasa suka sayi Phillppe Coutinho da Ousmane Dembele da kudin. Sannan kuma suka sayi Douglas da Prince Boateng, wadanda ba su tsinana wa kulob din komai ba.

Tun bayan tafiyar Johan Cruyff da Pep Guardiola, Barcelona ta saki kyakkyawan salon ta da duniya ta san ta da shi – wato salon a taka muku leda, a kunyata ku, kuma a jefa kwallo a ragar ku.

Sai kulob din ya fara take-taken neman ‘sa’a-dai-nasara-dai’ a karkashin Tata Martino, Luis Enrique da kuma Valverde wanda aka sallama jiya Litinin.

An san sabon kociya da sha’awar irin salon takun wasan da Cruyff da Guardiola suka koyar. Ya zama wajibi idan ya na so ya tsira da mutuncin sa, to ya ci gaba ko kuma ya dawo da irin na su salon, ko kuma kafar sa ta kai shi inda ya fito, tun lokacin tafiyar sa bai kai ga yi ba.

Babbar akidar da Guardiola ya rike, kuma ta kai shi ga nasara, ita ce La Masia, wato kyankyashewa, raino da kuma yaye kananan yara daga karamin kulob din Barcelona zuwa babban kubob. Sai kuma dauko kananan yara daga wani wuri a raine su a kulob din.

Hana rantsuwa Luis Enrique ya raini Sergi Roberto, shi kuma Valverde ya raini Ansu Fati. Amma kananan yara hatsabibai irin su Carle Alena da Dani Olmo, sun kauce tun da aka bada aron su, ba su sake komawa Barcelona ba.

Tun bayan tafiyar Guardiola sai wannan salo ya shiririce, iyayen yara suka rika korafin cewa ba su sanin halin da tasirin yaran su ke da shi. Wasu yaran kuma maimakon a shigar da su cikin babban kulob, sai aka rika tura su wasu kungiyoyi ana bada aro ko lamunin su.

Yawa-yawan yaran idan sun tafi, kowa sai ya kama gaban sa, ba ya sake komawa ta kan Barcelona.

Saurin Fushi Kan Abu Kadan

An dauki tsohon mai tsaron gidan Barcelona, Victor Valdes domin koyar da karamin kubob din Barcelona wasa, amma kwanan sa 80 kacal aka kore shi, saboda ya yin tankiya da Daraktan Koyar Da Kananan Yara Kwallo, wato Patrick Kluivert, wanda shi ma tsohon dan wasan Barcelona ne.

Ire-iren wadannan misalan su na da yawa. Kusan dalili kenan Carles Puyol, Jordi Cruyff da kuma a yanzu Xavi Harnendez suka yin baya-baya da aiki a Barcelona, a takaice har sai shugabannin da ke rike da kulob din sun kammalla wa’adin su, an zabi wasu tukunna.

Gwanitta da kwarewar Lionel Messi ta taimaka wa Barcelona tun bayan barin Guardiola daga kulob din.

Amma idan ka tsame Messi shi kadai daga Barcelona, to za ka ga sauran ’yan wasan kusan duk tubalin-toka ne.

Hausawa dai na cewa ‘komai darajar sa ke saida shi’. Shin ko Barcelona za ta yi dan-karen tsada a karkashin sabon kociya Sitien?
Mu dai sharhi ne na mu. Sannan kuma ’yan kallo ne mu, ba ‘yan wasa ba.

Tags: AbujaBarcelonaHausaLabaraiMadridNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

Dalilin da ya sa kotun Koli ta bayyana Hope na APC wanda ya lashe zaben Imo duk da ya zo na hudu

Next Post

RUNDUNAR AMOTEKUN: Dattawan Yarbawa sun maida wa Gwamnatin Tarayya raddi

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Amotekun

RUNDUNAR AMOTEKUN: Dattawan Yarbawa sun maida wa Gwamnatin Tarayya raddi

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • NASIHA: Ya Allah, Kayi Muna Tsari Da Girman Kai, Daga Imam Murtadha Gusau
  • CUTAR DIPHTHERIA: An samu ƙarin mutum 8,406 da suka kamu da cutar a jihohi 19 a Najeriya – NCDC
  • Za a sheka ruwan sama kamar da bakin kwarya cikin kwanaki uku masu zuwa a jihohi 18 a Najeriya – NiMet
  • Yadda Ƴan bindiga suka kashe mutum 9 a Avi Kwall, jihar Filato
  • Yadda abokai kuma ɗaliban jami’ar Dutsin Ma, suka kashe abokin su saboda budurwa

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.