Ka’idoji da sharuddan da aka gindaya, kamar yadda Ministan Harkokin Waje, Onyeama ya bayyana, sun hada da:
Duk wani kayan da za a shigar daga wata kasa da ke karkashin Kungiyar Kasashen Afrika ta Yamma (ECOWAS), to su kasance ba a farke kwalayen su ba.
Kayan su kasance jami’an waccan kasar sun rako su har bakin kan iyakar shigowa Najeriya. Su damka kayan ga jami’an kwastam na Najeriya kamar yadda kayan su ka fito daga kasashen da aka sayo su, ba tare da an farke kwalayen su ko an yi musu ribage ba.
Najeriya ba za ta amince ta yin kumbiya-kumbiya a wannan tsari ba.
Kayan da ake yi daga kasashen Kungiyar ECOWAS su kasance ingancin su ya kai sharuddan da ECOWAS ta gindaya.
Sannan kuma kayayyakin da za a rika shigowa da su daga kann iyakokin Najeriya, su kasance akasari kayayyaki ne da ake sarrafawa a cikin wadannan kasashe.
Kayan da za a shigo da su daga wasu kasashen da ba na ECOWAS ba, sun kasance ingancin su haura sharuddan na ECOWAS da kashi 30 bisa 100. Saboda kasashen ECOWAS tilas su karfafa cinikayya a tsakanin su.
Dole sai an rushe dukkan wasu manya da kananan rumbunan ajiyar kayayyaki da ke kan iyakokin kasashen da suka yi makwabtaka da Najeriya.
Tilas a rika daure kayan da za a shigo da shi a cikin kwalaye ko buhuna masu ingancim saboda ba kowane irin tarkace ne Najeriya za ta sake bari a shigo ma ta da shi daga wasu kasashe ba.
Duk dan wata kasar da zai shigo Najeriya ko wani wanda zai fita daga Najeriya, tilas ya kasance ya fita ko ya shigo kan iyakokin da aka amince a shigo. Kuma ya kasance ya kai kan sa wurin jami’an kula da shigi da fice da ke kan iyakar, kuma ya kasance ya na da takardun amincewa shigowa kasar nan.
Nan da makonni biyu Najeriya za dauki nauyin zaman nazarin wannan ka’idoji tare da wakilai daga Jamhuriyar Benin, Nijar da na Najeriya.
Shugabannin Ma’aikatun Harkokin Waje, Cikin Gida, Kudade, Kwastam, Shige-da-fice, Tsaro na NIA da sauran jami’an bangarorin tsaro na kowace kasashen uku za su kasance cikin wannan kwamiti.
DOKOKIN HANA ‘YAN KASASHEN WAJE KASUWANCI A GHANA
Dokar farko ta haramta wa ‘yan kashen waje gudanar da saye da sayarwa a cikin kananan shaguna ko kasa kaya a kan tebur ko yawon talla a ko’ina.
An haramta wa ‘yan kasar waje gudanar da tuka taxi a karkashin kamfanin zirga-zirgar da motocin da ke karkashin sa ba su kai 25 abin da ya yi sama ba.
Doka ta uku an haramta wa ‘yan kasar waje yi ko bude wurin yin kitso, karin gashi ko aski.
Doka ta hudu kuma an haramata wa ‘yan kasashen waje mazauna Ghana harkar buga katin waya su na sayarwa.
An kuma hana su buga litattafai da makamantan harkokin dab’i.
An hana su bude gidan sarrafa ruwan leda, wato ‘pure water’, kuma an haramta musu sayar da shi.
An kuma haramta wa baki ‘yan wata kasa ba ‘yan Ghana ba sayar da magunguna da bude shagunan sayar da magunguna (chemists).
An haramta musu gudanar da duk wani nau’i na cacar ‘lottery’, sai ta kwallon kafa kadai.
Discussion about this post