• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    Thugs-attack-collation

    ZAƁEN GWAMNONI YA ƊAU ZAFI: An kashe shugaban PDP bayan an lakaɗa masa dukan tsiya a rumfar zaɓen sa

    2023: Ya mutan Adamawa, ga Tinubu ga Binani na kawo muku su – Shelar Buhari a Yola

    ADAMAWA TA KWASHI ‘YAN KALLO: Binani ta kamo hanyar tururmusa ƙarti 14 a kokawar ƙwace kujerar gwamna

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: Muhimman Abubuwan Da Suka Faru Daga Ƙarfe 11 Zuwa 12:30 Na Ranar Zaɓe

    INEC ta dage zabe a rumfuna 10 a jihar Legas

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    Thugs-attack-collation

    ZAƁEN GWAMNONI YA ƊAU ZAFI: An kashe shugaban PDP bayan an lakaɗa masa dukan tsiya a rumfar zaɓen sa

    2023: Ya mutan Adamawa, ga Tinubu ga Binani na kawo muku su – Shelar Buhari a Yola

    ADAMAWA TA KWASHI ‘YAN KALLO: Binani ta kamo hanyar tururmusa ƙarti 14 a kokawar ƙwace kujerar gwamna

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: Muhimman Abubuwan Da Suka Faru Daga Ƙarfe 11 Zuwa 12:30 Na Ranar Zaɓe

    INEC ta dage zabe a rumfuna 10 a jihar Legas

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

DAN HAKIN DA KA RAINA: Yadda Amurka ke tsoron gabza karo da Iran

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
June 29, 2019
in Rahotanni
0
DAN HAKIN DA KA RAINA: Yadda Amurka ke tsoron gabza karo da Iran

Trump and Rouhani

A fili ta ke cewa kowa ya sani a duniya babu kasa mai karfin arziki da karfin makamai kamar Amurka. Sai dai kuma tabbatattun bincike-bincike da nazari da tsinkaye na nuna cewa Amurka na shayin haye wa Iran kai-tsaye, domin ko da ba ta iya kayar da ita, to za ta guntule mata kafa daya ko kuma hannu daya.

Hausawa kuwa sun dade su na cewa ‘dan hakin da ka raina shi ke tsone maka idanu.’ Watakila ma har ya iya makantar da idanuwan biyu.

Tun bayan da aka daina yakin-cacar-baki, baya ga kasar Koriya ta Arewa, babu wata kasa da ke fitowa gaba gadi ta na kalubalantar Amurka kai-tsaye kamar Iran.

A duk lokacin da Tehran ta samu dama, ba ta dage kafa ko sassautawa wajen caccakar Amurka musamman a duk inda ta ga Amurka din na wuce gona da iri wajen yin kaka-gida ko kane-kane a harkar tattalin arziki, siyasa, diflomasiyya, kisisisina, tuggu ko diflomasiyyar-kutunguiwa da algungumancin manyan kasashen duniya da Amurka ta sama yin katsalandan.

Tattalin kayan yakin da Amurka ke yi ta na girkewa a yankuna da kasashen da ke kusanci da Iran, musamman a cikin teku, ya na zama bazarana ga Iran.

Cikin shekarun nan, abin da Amurka ta kashe wajen makamai ya nunka tattalin arzikin Iran gaba daya.

A na ta bangaren, ita kuma Iran ta maida hankali wajen kara karfin makaman ta masu linzami wajen kara masu dogon zango da kara nauyin lodin bama-baman da za su rika dauka. Tare kuma da kara gyara musu saiti ta hanyar amfani da na’urorin zamani, yadda ko an harba ba su rika yin kuskure ba.

Hukumomin Tsaron Iran sun gamsu da kera makami mai linzami na zamani, wanda ya fi kowane mummunar barna. Suna kiran sa Shahab, wanda samfuri ne aka dauko daga Koriya ta Arewa.

YAKI SAI DA MAKAMI

Tabbas Amurka na tsoron mugan makaman Iran masu linzami samfuran SejjiI-1 da SejjiI-2. Iran ta taba gwada na farkon tun cikin 2008.

Ko a cikin 2009 a watan Nuwamba, sai da Sakataren Tsaron Amurka na lokacin, Robert Gates ya tabbatar da cewa makamin Iran samfurin SejjiI zai iya cin nisan kilomita 2,500 idan suka harba shi. Kuma zai isa cikin dan kankanin lokaci.

Shi ma Ministan Tsaron Iran, Mustafa Mohammed ya tabbatar da cewa SejjiI guda daya rak na iya daukar bam mai nauyin kilogram 750 ya je har cikin kasar Isra’ila ko wasu kasashen Turai ya jefa ya dawo.

Tsoron da Amurka da Turai da Isra’ila ke yi shi ne, kada wata rana Iran ta loda wa irin wannan makami mai linzami da bama-bamai na nukiliya ta cilla su Isra’ila ko wasu kasashen Turai.

Fitattun masana makamai na zamani na duniya sun tabbatar da cewa Iran ta gwada makamin SejjiI-2 cikin 2009. Kuma za a iya loda masa bama-bamai masu nauyin kilogram 650.

Sauye-sauyen karin inganci da suka yi wa wadannan tulin makamai a baya-bayan nan, an yi ittifakin cewa an yi musu garambawul ta yadda duk wanda aka harba, sai ya dangana da inda aka auna shi, ba tare da kuskure ba.

Sannan kuma kowane zai iya kai nisan zangon kilomita 2510, a cikin kankanin lokaci.

GHADIR, HATSABIBAN JIRAGEN KARKASHIN RUWA NA IRAN

Babban tsoron da manyan kasashen duniya ke wa Iran, musamman Amurka, shi ne yadda ta mallaki wasu hatsabiban kananan jiragen karkashin ruwa (submarines).

Ana kallo cewa wadannan barazana ce babba ga kasuwar hada-hadar danyen mai ta duniya. Domin kashi 20 bisa 100 na danyen mai da ake jigila da safara a duniya, sai ya bi ta Mashigar Ruwa ta Hurmuz, wato ‘Strait of Hormuz’.

Ana ganin idan daji ya yi dameji, to babu mai iya hana Iran ragargaje duk wani jirgin ruwan da ya bi ta wannan zirin hanyar ruwan teku zai gilma zuwa Turai.

Shi ya sa ma aka kiyasta cewa Amurka ta kashe sama da dala tiriliyan 8 daga 1976 zuwa yau, wajen kare wannan yankin ruwa na ‘Strait of Hormuz’, wato Mashigar Ruwa ta Hurmuz.

Cibiyar Nazarin Yaki ta Duniya (ISW) ta tabbatar da cewa Iran za ta iya aika kananan jiragen ta na yakin karkashin ruwa, dauke da muggan makamai su rika yin kwanton-bauta a kan duk wani babban jirgin da zai iya bi ta Tekun Arebiya, ta lalata shi.

Abin tsoron shi ne Iran ta mallaki irin wadannan kananan jiragen karkashin ruwa masu yawan gaske, kuma kowane ya na da nauyin tan 150. Sunan su Khadir ko Qadir, wadanda sun a da kamanceceniyar samfur da na Koriya ta Arewa masu suna Yugo da Sango.

Ko a cikin 2013, sai da Chris Harmer na cibiyar ISW ya ce wadannan jiragen karkashin ruwa na Iran abin tsoro ne matuka. Kanana ne, amma za su iya tarwatsa duk girman jirgin ruwa ko jirgin yaki na ruwa idan suka yi kwanton bauna a karkashin ruwa

YAKIN ’YAR-ROTOTUWA (drone)

Irin yadda dakarun kasar Iran suka harbo jirgin leken-asiri na kasar Amurka, ya tabbatar da cewa Iran ba kasar da Amurka za ta iya yi wa yadda ta ga dama ba ce. Kuma ta nuna wa Amurka cewa duk mai tsoron aradu, to shi ta ke fada wa.

Iran ta harbor jirgin nan na daukar bayanai mai sarrafa kan sa da kan sa, da aka fi sani da ‘drone’, wato ’yar-rototuwa. Ta kifo jirgin ne bayn ta leko shi ya na yi wa Amurka leken asiri a cikin kasar Iran.

Sai dai jirgin na ‘drone’ din na Amurka, ya sha bamban da duk wani jirgin rotutuwa na duniya, wajen girma da kuma tsada. An tabbatar da cewa Amurka ta kashe dala milyan 180 wajen kera shi. Kuma dauke ya ke da tulin bayanai na leke asiri kafin Iran ta kifar da shi.

MAKAMIN KHALIJ-E FARS (DILLALAN MUTUWA)

Iran ta tanadi tulin wasu kananan makaman linzami da ake harba wa a kan jiragen ruwa, wadanda ta rada wa suna ‘dillalan mutuwa’, kamar yadda ake yi musu kirari. Amma sunayen su a rubuce su ne ‘Khalij-e Fars (ASBM). Duk gudun jirgin ruwa, Iran na iya yin amfani da wadannan makamai ta kifar da su. Su na cin zangon kilomita ‘300 cikin kiftawa da bisimillah’.

Sannan kuma su na daukar bama-bamai masu nauyin kilogram 650. Sojojin ruwan Iran ne ke amfani da su. Kuma da na’ura suke aiki. Shi ya sa duk inda aka cilla su, to sai sun dangana.

Sannan kuma ana tsoron Iran za ta iya amfani da karfin da ta ke da shi a fadin duniya wajen masu goyon bayan ta, su rika kai wa Amurka da kasashen Turai hare-hare a wau kasashe. Musamman ana gudun Hezbollah da ke Lebanon, kan iyaka da Isra’ila.

Tags: AbujaAmurkaHausaHausa DuniyaIranIraqLa araiNajeriyaPREMIUM TIMES
Previous Post

INEC ta fi sauran hukumomin kasar nan kara samun inganci –Yakubu

Next Post

Jihar Gombe ta raba maganin ciwon kurkunu miliyan 7

Next Post
GOMBE STATE

Jihar Gombe ta raba maganin ciwon kurkunu miliyan 7

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Abubuwa 11 da ake so a yawaita yi a watan Ramadan
  • ZABEN KADUNA: PDP ta yi murdiya a wasu kananan hukumomi, zan Kalubalance su a Kotu – Uba Sani
  • SABUWAR ƁARAKA A PDP: An dakatar da Fayose, Anyim, Gwamna Ortom zai gurfana gaban kwamitin ladabtarwa
  • Yunƙurin ‘yan majalisar APC uku masu so a halasta tu’ammali da tabar wiwi ya samu cikas
  • ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Keyamo ya roƙi SSS su kama Obi da Datti, saboda furucin cewa ‘zaɓen 2023 daidai ya ke da mulkin soja’

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.