Shugaban jami’ar MAAUN dake Nijar da Najeriya, Farfesa Adamu Gwarzo ya kai wa shugaban kasar Nijar, Mohammed Bazoum ziyarar ta’aziyyar rasuwar sirikar sa, wato mahaifiyar mai ɗakinnsa, Hajiya Bintou.
Hajiya Bintou ta rasu a wani asibiti a kasar Faransa bayar fama da ta yi da ƴar gajeruwar rashin lafiya.
Hadjiya Bintou ta rasu ranar 29 ga Oktoba.
Farfesa Gwarzo ya ziyarci fadar shugaban kasar Nijar ranar Laraba inda ya mika ta’aziyyar sa sannan kuma da yi mata adduar Allah ya kyautata makwancinta, Amin.
” Wannan rahi ya shafe mu gaba ɗaya ne. Hadjiya Bintou ta yi rayuwa ne wanda kowa da ya santa zai yi alfahari da irin wannan rayuwa. Allah muke roko ya gafarta mata, sannan ya bamu duka jimurin hakurin wannan rashi da mukayi.
Shugaban kasar Nijar, Bazoum ya godewa Farfesa Gwarzo bisa wannan ziyara da ya kawo masa har gida don yi masa ta’aziyyar rasuwar mahaifiyar maiɗakinsa, Hajiya Bintou.
Discussion about this post