Bayan taron kaddamar da kamfen din takarar shugaban kasa da APC ta yi a garin Jos, ‘yan jam’iyyar PDP sun fito kwansu da kwarkwata ranar Talata inda suka dunguma filin wasa na Rwang Pam domin wanke ‘Kazantar APC’.
Darekta janar din Kamfen din kungiya ‘Tafiyar Atiku’ Kamru Sani ya shaida wa Kamfanin dillancin labaran Najeriya cewa magoya bayan PDp sun fito ne domin su wanke dauda da kazantar da APC ta kawo masu jihar Filato.
Ya kara da cewa jihar Filato ta PDP ce kuma wannan karon za su tabbatar wa mutanen Najeriya haka ta hanyar yi mata ambaliyar ruwan kuri’u.
” Mun fito ne domin mu wanke dattin da APC suka jibga mana a garin Jos. Za mu wanke garin tas, domin Filato ta PDp ce yanzo. Ragaraga za muyi wa APC tun kafin bullowar rana, ranar zabe.
Discussion about this post