A wani ƙawancen siyasa na wasu matasan ƴan siyasa da ludayinsu ke kan dawo da su ka fito daga mazaɓar ɗan majalisar dattawan kudancin Kano, inda su ka ɗauko wani gangami wanda a tunaninsu suke ganin za su ceto al’ummar wannan yanki daga wariya da kuma halin ko in kula da ake nuna masu a wajen fitar da shugabanni a jihar musamman ta ɓangaren zartarwa wato gwamna da mataimakinsa.
Dukkanin al’ummar dake wannan jiha na sane da cewa wannan yanki ya daɗe yana nema a ba shi dama domin fitar da ɗan takarar da zai zama gwamna a wannan jiha, sai dai kash hakan al’ummar wannan yanki ya gaza cimma ruwa.
Yankin Kano ta kudu a baya in mu ka yi duba za mu ga ya fitar da gwamnoni har guda biyu waɗanda suka mulki Kano wannan a tsari na dimokariya wato marigayi Alhaji Muhammad Abubakar Rimi da kuma Sanata Kabiru Ibrahim Gaya wanda a yanzu shi ne ɗan majalisar dattawa mai wakiltar wannan yanki.
Sai dai tun dawowar mulkin dimokaradiya a wannan jamhuriya ta huɗu yanki ke ta ƙishirwar neman ya samu ko da mataimakin gwamna ne amma abin ya ci tura. A yanzu dai zamu iya cewa yau shekara 23 da dawowar wannan jamhuriya amma yankin Kudancin Kano bai amfana da komai ba sai kakakin majalisar dokoki.
Bari mu ɗan yi duba da shugabannin da suka shugabanci jihar Kano daga 1999 zuwa yau. A farkon dawowar dimokuraɗiyya a wannan jamhuriya, Engr. Rabi’u Musa Kwankwasao wanda ya fito daga Kano ta tsakiya ya jagoranci jihar har tsawon shekara huɗu daga shekarar 1999 zuwa 2003 tare da Dokta Abdullahi Umar Ganduje a matsayin mataimakinsa wanda ya fito daga yankin Kano ta Arewa.
Bayan haɗa wa’adin mulkinsa na shekara huɗu sai Malam Ibrahim Shekarau ya kayar dashi a zaɓen 2003, wanda daga nan ya riƙe jihar har tsawon shekara takwas (2003 – 2011).
Malam Ibrahim Shekarau a lokacin mulkinsa yayi mataimaka guda biyu wato marigayi Engr. Magaji Abdullahi sai kuma Engr. Abdullahi Tijjani Muhammad Gwarzo waɗanda dukkaninsu sun fito daga yankin Kano ta Arewa. Bayan kamala wa’adin na su ne, sai Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso ya sake dawowa a karo na biyu tare da mataikinsa na waccan lokacin Abdullahi Umar Ganduje inda ya karasa zango na biyu na mulkinsu.
Hakazalika, bayan kammala wa’adin mulkin na Kwankwaso ya zaɓi mataikinsa a matsayin wanda zai gaje shi inda ya haɗa takararsu da Ferfasa Hafizu Abubakar, sai dai Farfesa Hafizun bai ƙarasa wa’adin mulkin ba bayan samun wani saɓani da gwamnan na Kano inda ya ajiye aikin nasa.
Daga nan a shekarar 2018 sai Gwamna Ganduje ya zaɓi kwamishinansa na harkokin noma, Dokta Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin wanda zai maye gurbin Farfesa Hafiz, wanda da shi ne ake sa ran za su ƙarasa wa’adin mulkin na su. Dukkanin waɗannan mataimaka na Gwamna Ganduje sun fito ne daga Kano ta tsakiya.
Wannan wariya da ake nunawa wannan yanki na kudancin Kano a siyasar jihar a wannan lokaci, shi ne ya zaburar da wasu jigogi a yanki suka haɗa wata tafiya da suke kira da “Yan Ukun Baba Ganduje” domin su fitar da yanki daga wannan ƙangi na siyasa da su ke ciki.
Jagorori a tafiyar sun haɗa da tsohon kakakin majalisar dokokin jihar Kano kuma ɗan majalisa da ke wakiltar al’ummar Rano, Kibiya da Bunkure a majalisar ƙasa a halin yanzu wato Kabiru Alasan Rurum, sai tsohon wakilin al’ummar Sumaila da Takai a majalisar tarayya, Sulaiman Abdurrahman Kawu Sumaila da kuma shugaban masu rinjaye a majalisar tarayya kuma wakilin al’ummar Tudun Wada da Doguwa, Alhasan Ado Doguwa.
Wannan tafiya dai tun kafin ta yi nisa masana da dama sun yi haashen cewa ba inda za ta je duba da wasu dalilai, musamman idan aka yi la’akari da son zuciyar wasu daga cikin jagororin.
To amma dai za mu iya cewa tafiyar a baya ta fara armashi domin kuwa an hango jagororin a lokuta da dama suna taro domin shawo kan matsalar ta su inda su ke neman fito da ɗaya daga cikinsu domin neman takarar gwamnan Kano a kakar zaɓen shekarar 2023.
Dukkanin alamu sun yi nuni da cewa Kabiru Alasan Rurum shi ne wanda za su sanya a gaba. Sai dai kamar yanda alamu su ka yi nuni, da yawa daga cikin masu fashin bakin siyasar Kano sun tabbatar da cewa tafiyar ba za ta yi nisa ba, duba da irin mutanan da aka haɗa a tafiyar.
Sanin kowa ne cewa waɗannan ƴan siyasa su na da mabambantan ra’ayi sannan suna da son kansu fiye da ta al’ummarsu. Wanda hakan ne ta sa akai hasashen cewa za su iya fifita buƙatarsu akan ta al’ummar yankin, sai ga shi kuwa hakan ce ta kasance a ƙarshen tafiyar.
Rugujewar ƙawancen siyasar ya faru ne bayan da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya furta cewa zai goyin bayan mataimkinsa tare da tsohon kwamishinan ƙananan hukumomi a kakar zaɓe mai zuwa. Wannan furuci na Gwamna ya sanya al’umma tunanin cewa zai harzuƙa dukkanin jagororin wannan tafiya, sannan su ɗauki matsaya guda ɗaya tare, sai dai kash sai aka jiyo ɗaya daga cikinsu wato Alhasan Ado Doguwa na alakanta kan sa da wannan zaɓi na Gwamna.
Tuni dai aka rasa shugabanni biyu daga cikin tafiyar, domin tuni sun fice daga jam’iyyar APC akan zargin rashin adalci daga Ganduje. Sai dai a iya cewa Alhasan Ado Doguwa ya maƙale a baya, ya zaɓi fifita buƙatarsa akan ta al’ummar yanki Kano ta Kudu.
Ali Sabo Dan Jarida ne kuma mai sharhi akan al’amuran yau da kullum. Ya rubuto daga Kano. Za a iya samun sa akan adireshinsa na imel aliyuncee@gmail.com
Discussion about this post