Tsohon shugaban Cibiyar Kasuwanci da Masana’antu na jihar Legas Muda Yusuf ya nuna rashin jin dadin da yadda farashin iskar gas ka kara hauhau a kasar nan.
Muda ya koka kan yadda iskar gas ke ci gaba da tashin gwauron rabi a kasar na kamar ba a kasar ake hako da sarafa iskar gas din ba.
” ‘Yan Najeriya na cikin tashin hankali matuka. Abinci ya na neman ya fi karfin talaka saboda dan karan tsada da yayi, sannan kuma Gas din da ake samu a dafa abinci ya zama bala’i a kasa. Kusan duk mako sai farashin tukunyar Iskar gas tashi.
” Tukunyar Iskar Gas mai nauyin Kilogiram 12.5 yanzu ana saida shi naira N9300 a kasuwa. Dama gas din ne mafi yawan yan Najeriya ake amfani da shi ana girki. Talaka mai karamin Karfi sai ya siya yar karamar tukunya ya rika maneji amma kuma saka iskar gas din ya zame sai dai hange daga nesa.
Yusuf ya kara da cewa, mutane sun koma sai sarar itatuwa a ke yi domin girki a gidaje. Abinda ba haka ya kamata a yi ba.
” Ya kamata ace tunda Najeriya na da isasshen iskar gas har tana fitarwa kasashen waje, ya kamata a ce a gida ‘yan kasa da samunta
Discussion about this post