• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125

    Kotu ta kwato maka-makan gidaje 48 a hannun tsohuwar Shugabar Hukumar NSITF

    KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu

    Gwamna Uba Sani ne ya yi  Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    Gwamna Uba Sani ne ya yi Ruwa ya yi Tsaki a takara ta ba mahaifina El-Rufai ba – Bello El-Rufai

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    FALLASA RUFA-RUFAR HADI SIRIKA: Majalisar Tarayya ta nemi Gwamnatin Tarayya ta dakatar da Nigeria Air

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Sanata Wamakko ya yi tir da kisan kiyashin da aka yi a tangaza, jihar Sokoto

    Atiku ya kafa gaggan lauyoyi 18, ya ce su tashi tsaye su ƙwato masa ‘nasarar zaɓen sa’ daga hannun Tinubu

    SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Atiku ya zargi INEC ta ƙin ba shi kwafen bayanan zaɓe duk da ya biya haƙƙin Naira miliyan 6 kuɗin karɓar bayanan

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

RIKICIN APC A KANO: Tsakanin Ganduje da Shekarau wanene zai yi nasara? Daga Buhari Abba

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
November 12, 2021
in Ra'ayi
0
RIKICIN APC A KANO: Tsakanin Ganduje da Shekarau wanene zai yi nasara? Daga Buhari Abba

Jam’iyyar APC a jihar Kano da ke Najeriya na ci gaba da fama da rikicin cikin gida, wanda ya samo asali tun kafin gudanar da zabukan shugabannin jam’iyyar a matakin mazabu da jiha da aka aiwatar baya bayan nan.

Tun da farko dai Sanatan Kano ta tsakiya Malam Ibrahim Shekarau da takwaransa na Kano ta Arewa da sauran wasu ƴan majalisun wakilai guda huɗu ne suka gudanar da wani taro na musamman inda suka yanke shawarar lallai dole shugabancin jam’iyyar ta APC ya takawa Gwamna Abdullahi Umar Ganduje birki kafin lamura su ƙarasa dagule.

Bayan kammala taron ne ɓangaren Sardaunan Kano da na Gwamna Abdullahi Umar Ganduje su ka gudanar da zaɓukan jami’yyar a matakin jiha.
Ɓangaren Gwamna Abdullahi Umar Ganduje su ka zaɓi Alhaji Abdullahi Abbas Sanusi a matsayin shugaban jam’iyyar, yayin da ɓangaren Malam Ibrahim Shekarau su ka zaɓi Alhaji Ahmadu Haruna Zago a matsayin shugaban jam’iyyar ta APC.

Tasirin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje A Siyasar Kano

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ɗan siyasa ne kuma tsohon gogaggen ma’aikacin gwamnati. Masanin mulki a ilimance da a aikace, ya yi kwamishina har sau biyu, sannan kuma ya yi mataimakin gwamna shi ma sau biyu da sauran wasu muƙamai yanzu kuma yana matsayin gwamnan Kano.

Da yawan mutane na kallon Ganduje a matsayin mutum ne shi mai haƙuri da kawaici da kuma biyayya ga duk wanda ya grime shi ta kowacce fuska wanda ka iya kasancewa girma na shekaru ko na harkar aiki. Sai dai kuma makusantansa da abokan siyasarsa na yi masa shaidar rashin tsayawa akan magana ɗaya musamman a al’amuran da su ka shafi siyasa.

Gwamna Abdullahi Umar ya fara siyasa tun a jamhuriya ta biyu, inda ya shiga jama’iyyar National Party fo Nigeria (NPN). A wannan jama’iyyar ya riƙe muƙamin mataimakin sakatare na jihar Kano daga 1979 zuwa 1980. Ya sake shiga jama’iyyar PDP a shekarar 1999, ya kuma canja sheƙa tare da gwamnansa Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso, inda suka fice daga jama’iyyarsu ta PDP suka koma sabuwar jama’iyyar haɗaka ta APC, wanda a ƙarƙashin tutar wannan sabuwar Jama’iyyar ya samu nasarar cin zaɓensa na gwamna.

Tarihin siyasar Abdullahi Umar Ganduje ya nuna cewa ya tsaya takarar Kujerar Gwamnan jihar Kano a shekarar 1999, inda daga baya aka yi musu sulhu ya janye ya barwa tsohon Gwamna Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, wanda shi kuma daga baya ya ɗauke shi a matsayin mataimakinsa.

Bayan kammala wa’adin mulkin gwamnatin Rabi’u Musa Kwankwaso a shekarar 2015, Abdullahi Umar Ganduje, ya sake tsayawa takarar gwamnan Kano a ƙarƙashin tutar jama’iyyar APC. Ya kuma yi nasara kan abokin adawarsa a babban zaben, Malam Salihu Sagir Takai da kuri’a 1,546,434 yayin da Takai ya samu kuri’a 509,726 a zaɓen 11 ga watan Afrilun 2015.

Sai dai duk da wannan tarihin siyasar na Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, masu sharhi akan al’amuran da su ka shafi siyasar Kano na yi masa kallon ɗan siyasar da ba shi da gida na kan sa. Haka kuma ana kallon waɗanda su ke zagaye da shi su na binsa ne kawai domin yana rike da mulki.

Wani abin da masu sharhin ke ƙara buga misali da shi game da Gandujen shi ne mafi yawan waɗanda su ke cikin gwamnatinsa su na da ra’ayin Kwankwasiyya ko kuma ba sa tare da Gandujen ɗari bisa ɗari, musamman idan aka yi la’akari da yadda jami’an gwamnati da ƴan Gandujiyya su ka gaza taɓuka komai a lokacin zaɓen shekarar 2019, inda lamarin ya kai gwamnan shiga zaɓe zagaye na biyu.

Wani ƙarin misalin shi ne yadda gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya gaza samun cikakken goyon al’ummar ƙaramar hukumarsa ta haihuwa wato Dawakin Tofa, domin mafi yawan al’ummar wannan ƙaramar hukuma musamman matasa ba sa tare da shi a harkokin siyasa.

Su Wanene Su Ke Tare Da Ganduje?

A zahiri babu wani ɗan siyasa da ke da jama’a a jihar Kano kamar Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, domin shi ke da mafi yawan ƴan majalisar dokokin jihar Kano da kwamishinoni da ƴan majalisar wakilai da Sanata guda ɗaya (Kabiru Ibrahim Gaya), da shugabannin ƙananan hukumomi da Kansiloli da kuma masu ba shi shawara.

Haka kuma yana da ƙarfin gwamnati wanda ba wasa ba ne, domin ta na da matuƙar ƙarfi da tasiri akan dukkanin wani abu da ta sanya a gaba. Amma kaso mai yawa na waɗanda su ke tare da Gandujen da masu riƙe da muƙaman siyasa sun kasance masu fuska biyu. Ma’ana a zahiri su na tare da Gandujiyya a ɗaya ɓangaren kuma su ne ke mata zangon ƙasa wanda hakan babbar matsala ce a harkokin siyasa har da rayuwa gaba ɗaya.

Tasirin Malam Ibrahim Shekarau A Siyasar Kano

Malam Ibrahim Shekarau, tsohon malamin makaranta ne kuma masanin fannin karantarwa da harkar ilimi, gogaggen ma’aikacin gwamnati kuma fitaccen ɗan siyasa, mutum ne shi mai haƙuri da sauƙin hali da kirki da kuma biyayya ga duk wanda ke gaba da shi, a shekaru ko kuma a mulki, wanda hakan ya ba shi ɗimbin magoya baya a jihar Kano da ma wasu sassan Arewacin Najeriya.

A lokacin da Malam Ibrahim Shekarau ya shigo cikin siyasar jihar Kano gadan – gadan ba’a ɗauke shi a matsayin wani ɗan takara da zai yi tasiri ba a zaben gwamnan da aka yi a shekarar 2003 a jihar, amma daga baya kuma sai ya yi tasiri inda ya lashe zaɓen.
Lashe wannan zaɓen da Malam Shekarau ya yi ya jawo hankalin al’ummar Najeriya tare da jefa mamaki akan yadda Malamin makaranta da ke jam’iyyar adawa ya kayar da gwamna mai ci.

A ɓangare guda kuma Malam shekarau ɗin ya kafa tarihi inda ya zama gwamna na farko da aka zabe shi a karo na biyu a matsayin gwamna a tarihin jihar Kano.

Salon mulkin Malam Ibrahim Shekarau a lokacin da ya ke mulkin jihar Kano, salon gwamnati ne da ya haɗa dukkanin bangarorin al’umma. Domin a lokacin da ya ke gwamnan Kano ya baiwa ƙananan hukumomi haƙƙinsu ta yadda arziki ya wadata a tsakankanin al’ummar jihar Kano. Ya shigo da Sarakuna da Malamai da Ƴan boko da talakawan jihar Kano cikin gwamnatinsa.

Wannan salon gwamnatin Malamin gwamnan ta janyo masa farin jini daga ɓangarori daban-daban na al’umma. Domin a lokacinsa ko masu ƴan jam’iyyar adawa sai da su ka tsuke bakinsu saboda suma an tsoma su a cikin gwamnati.

Su Wanene Su Ke Tare Da Malam Shekarau A Siyasar Kano?

Malam Ibrahim Shekarau a siyasar jihar Kano yana da tasiri ƙwarai da gaske musamman a tsakankanin ma’aikatan gwamnati a matakin jiha da ƙananan hukumomi. Haka kuma a kafatanin ƙananan hukumomin jihar Kano 44 babu inda babu masu ra’ayin siyasar Malam Ibrahim Shekarau na haƙiƙa wadanda su ke yi ba domin kuɗi ba sai domin aƙida da yarda siyasar Malamin.

A ɗaya ɓangaren kuma gidan siyasar Sardaunan Kanon ya ƙara ƙarfi a sakamakon dawowar Sanata Kano ta Arewa, Sanata Barau Ibrahim Jibrin da Injiniya Tijjani Abdulkadir Jobe ɗan majalisar wakilai mai wakiltar ƙananan hukumomin Dawakin Tofa da Rimin Gado da kuma Tofa da Barista Haruna Isa Dederi ɗan majalisa mai wakiltar Karaye da Rogo da Nasiru Abduwa Gabasawa da Sha’aban Ibrahim Sharada da wasu daga cikin ƴan majalisar dokokin jihar Kano, wanda har yanzu ba su filto fili sun jaddada goyon bayansu ga tafiyar Malam Ibrahim Shekarau ɗin ba.

Baya ga wadannan ƴan majalisun akwai fitattun ƴan siyasar da aka san su akan tsayawa akan ra’ayin abin da su ka yi imani da shi a fage irin na siyasa. Wasu daga cikin wadannan ƴan siyasa ana yi musu kallon masu ra’ayin ƴan mazan jiya da su ka ƙware wajen rigimar siyasa. Fitattu daga cikinsu akwai Alhaji Ahmadu Haruna Zago da Abdulmajid Danbilki Kwamanda da Alhaji Shehu Ɗalhatu, da Alhaji Murtala Alhassan Zainawa da Kwamared Alhassan Uba Idris da kuma Alhaji Sharu Baban Lungu.

Tabbas wannan shata layi da ɓangarorin biyu su ka yi a cikin jam’iyyar APC zai iya zama dalilin wargaza jam’iyyar tsintsiya, wanda kuma hakan kan iya haifar da gaza lashe madafun iko a zaɓen shekarar 2023 a jihar Kano.

Lokaci shi zai tabbatar da wanene zai yi nasara a wannan kokawar siyasar!

Buhari Abba ya rubuto daga Kano – buhariabba57@gmail.com

Tags: AbujaGandujeHausaIbrahim ShekarauKabiru GayaKanoLabaraiMajalaisaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

SHIRIN MAGANCE AFKUWAR BALA’O’I: Nijeriya ta jaddada sadaukarwa ga yarjejeniyar Sendai a taron COP26 -Minista Sadiya

Next Post

TSADAR ISKAR GAS: Ina talaka zai sa kansa, Abinci ya yi tsada, abin dafa shi yayi tsada – Muda Yusuf

Premium Times Hausa

Premium Times Hausa

Next Post
TSADAR ISKAR GAS: Ina talaka zai sa kansa, Abinci ya yi tsada, abin dafa shi yayi tsada – Muda Yusuf

TSADAR ISKAR GAS: Ina talaka zai sa kansa, Abinci ya yi tsada, abin dafa shi yayi tsada - Muda Yusuf

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • HAJJI 2023: Hukumar Alhazai ta gindiya sabbin sharuɗɗan adadin kwanakin ziyara Madina
  • HANYAR DAMATURU ZUWA BIU: Yadda matafiya ke cin kwakwa Tsawon shekaru 9 an kasa kammala gyaran titin kilomita 125
  • KARKATAR DA NAIRA MILIYAN 289: EFCC ta gurfanar da wasu jami’an gwamnatin Katsina a kotu
  • DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad
  • SHARI’AR ZABEN SHUGABAN ƘASA: Kotu ta karɓi sakamakon zaɓen jihohi 17 daga hannun Peter Obi domin tantance sahihancin su

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.