Shugaban Kungiyar Likitocin Babban Asibitin Jami’ar Ibadan (UCH), Temitope Husein, ya bayyana cewa sun shiga cikin sahun yajin aikin da uwar kungiyar su ta likitocin Najeriya NARD ta shirya, saboda likitoci abokan aikin su 17 ne su ka rasa rayuwar su sakamakon aikin kula da masu cutar korona.
Hussein a kokarin san a nuna wajibcin tafiyar da su ka yi yajin aiki a karkashin kuniyar likitoci ta kasa Nard, ya bayyana cewa tun bayan mutuwar likitocin 17, har yau iyalan su ba su samu kudaden inshora din da ake bai wa iyalan mamacin da ya mutu a wurin aiki ba.
Ya kara da cewa likitocin sun tafi yajin aiki ne domin neman a biya su hakkin su da aka danne wa wasu yan uwan su likitoci a kasar nan.
Hakkokin sun hada da albashin da wasu ke bi har yau ba a kai ga biyan su ba, sannan kuma akwai alawus-alawus da kuma bukatar da su ke da ita na kara masu alawus din saida rayukan su da su ke yi da sauran su.
Ya nuna matukar damuwa da korafin cewa wasu likitocin su na fama da kuncin rayuwa sakamakon kin biyan su albashi, tsawon watanni uku da har yau su ke jira, ba a biya su ba.
Hussein ya kara da cewa likitoci sun bai wa Gwamnatin Tarayya isasshen lokaci na watanni uku domin su duba lamarin naira 5,000 kacal da ake bai wa likita matsayin kudin alawus din saida rai da ya ke yi. Amma har yau ba a kara masu ba.
Ya nuna haushin cewa a baya sun bai wa gwamnati wa’adin kwanaki 60, amma ba ta yi komai ba. “Kuma tun a ranar 25 Ga Janairu wannan wa’adin ya kare. Mun tafi yajin aiki ne saboda aiki mu ke yi, amma babu lada, sannan babu Allah bada lada.” Inji Hussein.
PREMIUM TIMES ta buga labarin tafiya yajin aikin da likotocin Najeriya su ka yi, kwanaki biyu bayan Buhari ya tafi neman ta sa lafiyar a Landan.
Kungiyar Likitocin Najeriya ta shiga yajin aikin game-gari, kwana biyu bayan da Shugaba Muhammadu Buhari ya tafi kasar Ingila domin ganin likitocin sa.
Kokarin da gwamnatin Tarayya ta yi domin shawo kan lamarin, ta hanyar kiran taron sasantawa da Ministan Kwadago, Chris Ngige ya yi da shugabannin kungiyar likitocin ta NARD a ranar Laraba, bai haifi da mai idanu ba, domin taron bai hana likitocin tafiya yajin aiki ba.
“Mun fara yajin aiki tun daga yau Alhamis karfe 8 na safe, yayin da a gefe daya kuma mu na nazarin tayin da gwamnatin tarayya ta yi mana”. Inji Shugaban Kungiyar Likitocin Najeriya, Uyilawa Okhuaiheuyi da a Turance a ke kiran ta da suna NARD.
Wannan furucin da ke sama, shugaban ya yi shi ne ga wakilin PREMIUM TIMES a safiyar Alhamis.
Kungiyar Likitocin Najeriya ta yi barazanar tafiya yajin aiki muddin gwamnatin tarayya ta kasa biya masu bukatun su, ciki kuwa har da biyan su hakkokin su na alawus-alawus da su ke bi ba a biya su ba.
Sun tafi yajin aikin ne a daidai lokacin da Shugaba Muhammadu Buhari ya tafi Ingila, domin likitocin sa a Landan su duba lafiyar sa.
Fadar Shugaban Kasa ta bayyana cewa ba wani bakon abu ba ne don Buhari ya tsallake daga Najeriya ya tafi Ingila ganin likita.
“Buhari ya shafe shekaru 30 ya na zuwa ganin likitan sa a Landan.” Inji Kakakin Yada Labarai na Shugaba Buhari, wato Malam Garba Shehu.
Shugaban na NARD ya ce dama sun bai wa gwamnatin tarayya wa’adin a biya masu bukatu kafin ranar 31 Ga Maris ta wuce. Don haka tunda ta wuce din ba a biya masu ba, shi ya sa su kafaa yajin aiki daga ranar Alhamis, 1 Ga Afrilu, 2021.
Wadannan likitoci da ke kan amun horon zama cikakkun manyan likitoci, su ne mafiya yawa a asibitocin kasar nan.
Abubuwan Da Su Ke Bukata Daga Gwamnatin Tarayya:
Su na o a biya su kudaden albashin su na baya da ba a biya su ba. Su na bukatar a sake duba kankantar kudaden alawus din saida rai da ake biyan u. Sun nemi wannann alawus na saida rai ya kai kashi 50 bisa 100 na adadin kudin albashin kowa.
Sannan kuma su na bukatar a biya su kudaden alawus-alawus na aikin korona da su ka yi wadanda har yau bayan saida rayuka da su ka yi wajen kokarin dakile korona da kula da masu dauke da ciwon korona, har yau ba a biya su alawus din ba, musamman ma likitocin da su ke aiki a karkashin manyan asibitoci na jihohi.
Discussion about this post