Sakatariyar yaɗa labaran gwamna Abubakar Bello na jihar Neja, Mary Noel-Berje ta bayyana wa manema labarai a garin Minna cewa mahara sun saki fasinjojin NSTA da suka yi garkuwa da su.
Idan ba a manta a cikin makon jiya ne mahara suka sace fasinjojin motar NSTA a hanyar Zungeru zuwa Minna.
Maharan sun yi ikirarin ba za su saki fasinjojin ba sai gwamnati ta biya su kudin fansa har naira miliyan 500 kafin su sake su.
A wani bidiyo da suka fitar maharan sun rika nuna karfin makaman su suna yi wa gwamnati izgilanci da yi musu kuri cewa ba za su saki fasinjojin ba.
Discussion about this post