• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

RAHOTON MUSAMMAN: Sunayen Wadanda Suka Durkusar da ‘Nigeria Airways’ kuma suka narke cikin gwamnatin Buhari

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
October 29, 2018
in Rahotanni
0
Nigerian Airways

Nigerian Airways

Ranar Talatar da ta gabata ne Majalisar Tarayya ba ta yi wata-wata ba, ta gaggauta zartas da kwamitin binciken yadda aka durkusar da kamfanin zirga-zirgar jiragen sama na ‘Nigeria Aiways’, wanda aka fara biyan kudaden fanshon tsoffin ma’aikatan kamfanin, mallakar Gwamnatin Tarayya.

Bayan an shafe makonni ana aikin tantance tsoffin ma’aikatan, an kididdige har mutane 6,000 da za a biya jimillar naira biliyan 45, wadanda ba a taba biyan su ko sisi ba, tun daga 2003, shekarar da kamfanin ya durkushe kasa warwas.

A can baya, gwamnatin Olusegun Obasanjo ta taba kafa kwamitin bincike a cikin 2002, a karkashin Mai Shari’a Obiora Nwazota, wanda ya gano cewa wasu mahandama sun wawure naira bilyan 60 na kamfanin.

Wancan kwamiti ya shawarci Gwamnatin Tarayya ta yi amfani da jami’an ‘yan sanda ta kwato kudaden da aka wawure, daga hannun mahandan, kuma a gurfanar da su kotu, musamman tunda su na raye, ana ganin su a kasar nan sai fantamawa suke ta yi.

JERIN CARBIN ‘YAN HARKALLA

Cikin shekaru tamanoni, wato farkon 1980 zuwa 1985, Nigeria Airways ya mallaki jirage, 32. Amma ya zuwa 2002, 30 sun lalace, ko kuma an wofintar da su, wasu an saida su, saura guda biyu kacal.

Wannan ne ya sa Obasanjo ya kafa kwamitin da aka dora wa nauyin bin diddigin yadda aka kashe ko da taro da sisi ne a kamfanin, ta hanyar binciken takardu da rasidan biyan kudade da kuma kididdigar kudaden da ke shiga.

Kwamiti ya shafe shekara daya cur ya na aiki, inda a karshe ya fita da wani shirgegen kundin da ya tattara bayanan yadda aka cinye kudaden kamfanin. Kundin wanda saboda girman sa, an buga shi ne har juzi’i hudu.

An samu jami’an kamfanin, kamfanonin ejan na zirga-zirga, bankuna, kamfanonin cikin gida da na kasashen waje da hannu dumu-dumu cikin wannan harkalla.

Tun a ranar 11 Ga Disamba, 2002 da Majalisar Zartaswa ta umarci Sakataren Gwamnatin Tarayya a yi amfani da jami’an tsaro a karbo kudaden tare da hukunta masu laifi, har yau ba a kara tada maganar ba.

YADDA AKA RIKA SAIDA SASSAN JIRAGE GA ’YAN JARI-BOLA

Bincike ya tabbatar da cewa jami’an Nigeria Airways babu ruwan su da bin ka’ida, sun sace milyoyin daloli, sun rika bada kwangilar bogi, an rika narka makudan kudade a wasu bankunan da tuni sun durkushe.

Wani babban abin firgitarwa kuma shi ne yadda aka rika yi wa kantama-kantaman jirage farashin cinikin huhun goro, da kuma yadda aka rika balle kangarwar fika-fikai da sauran sassan jiragen ana saida wa ’yan rafta, wato jari bola.

Yayin da manyan jami’an kula da kamfanin suka rika jefa kudaden shiga da riba a cikin aljihun su, sun kuma rika karbar makudan kudade a bankuna a matsayin kamfani ne ya karbi bashi, amma sai su jidi kudaden su nausa cikin gidajen su.

GANI YA KORI JI: SUNAYEN WADANDA SUKA KARYA NJIGERIA AIRWAYS: Manyan cikin su na da kusanci da Buhari

1. Mohammed Joji

– Bayan da ya wawuri kudaden ya cika cikin sa, Mohammed Joji, wanda shi ne tsohon Babban Daraktan kamfanin, sai ya kafa Skypower Express Airways.

– Kwamitin bincike a lokacin ya bada shawarar cewa a haramta masa sake rike wani mukami a Najeriya, ko da kuwa manajan gidan wanka da bahaya ne.

– An kama Joji ya jidi naira biliyan 4.37 a cikin 1993 kacal, watau dala milyan 12 wadda kamfanin jirage na Swissair ya biya kudin ladar sauka da tashi ga Nigeria Airway, kuma Joji ya ragargaje kudaden.

– Ya karkatar da wata dala milyan 9.8, wadda ya ce wai ya biya Sabena Airline na Belgian. Bincike ya nuna cewa dala milyan daya kacal ya ba su.

– Akwai wata harkallar dala milyan 3.53, sai wata dala milyan 2.45, da kuma wata dala milyan 2.20 wadda ita ma aka ce ta yi fika-fiki ta tashi sama.

– A takaice a cikin watanni 24, Joji ya jidi dala milyan 30.018, watau sama da naira bilyan 11.

Sai dai kuma da PREMIUM TIMES ta tuntube shi, ya ce laifukan da aka ce ya yi duk bi-ta-da-kulli ne Ministar Harkokin Sufurin Jirage ta Loakacin Obasanjo, Kema Chikwe ke yi masa.

Sai dai kuma abin takaici, gwamnatin Muhammadu Buhari ta nada shi shugabancin kwamitin fadada aikin titin filin jiragen sama na Abuja, kuma shi ne shugaban shirin maida jiragen Abuja sauka Kaduna a lokacin da ake aikin gyaran filin Abuja.

2. JANI IBRAHIM: JANI YA JA KAYA

A yanzu dai Jani su ne manyan ’yan jam’iyyar APC na jihar Kwara, ya yi shugabancin Nigeria Airways tsakanin 1996 zuwa 2001. Watau kenan su ne suka karasa binne gawar jiragen a rami, tunda a cikin 2002 ya durkushe.

A yanzu Jani darakta ne a Heritage Bank. Kwamitin bincike ya rubuta cewa: “Jani bai taba bada wata kwangila ba tare da ya yi harkalla a cikin ta ba.” An kara bayyana shi a matsayin “dan harkalla ne lamba daya.”

Rahoton kwamiti ya ce Jaji ya maida kudin kamfanin kamar gadon gidan su, kuma duk wanda ya ga zai iya kawo masa barazana, sai kawai ya kore shi daga kamfanin.

– Tsakanin 1997 zuwa 1999 ya cinye naira biliyan 1.47.

– Akwai kuma wata dala milyan 1.7 da kuma dala miliyan 1.2

– Gaba daya dai naira bilyan 3.63 ake nema a hannun sa, wadanda aka rasa yadda aka yi da su.
– Sai kuma wasu filaye 22 da ya raba wa wasu mutanen da ba ma’aikatan Nijeria Airways ba ne.

3. BERNARD BANFA Da PATRICK KOSHONI: ABOKIN DAMO GUZA

Dukkan su tsoffin manyan jami’an sojojin sama ne da suka yi ritaya. Banfa ya yi shugabancin kamfanin bayan ya yi ritaya daga aikin soja. Shi da Koshoni abokan cin mushe ne, ba mai boye wa kowa wuka kenan. tafiyar su daya, kuma tare suka yin harkalla.

– Su biyun sun hada baki, sun ciccibi girgi daya, kirar A310, suka saida a farashi mai rahusa, bayan an ba su shawarar kada su yi haka. Kwamiti ya ce su maido naira bilyan 158, watau dala miyan 435 na kudin wancan jirgi da suka sayar.

YADDA BUHARI YA NADA ’YAN HARKALLA CIKIN GWAMNATIN SA

– Babu wani tabbacin cewa su Banfa sun biya kudaden, amma dai abin da ya biyo baya shi ne, Banfa ya shiga tawagar guguwar Buhari ta CPC, wadda ta narke cikin APC a yanzu.

– Cikin 2016 Buhari ya yi wa Banfa sakayyar nada shi cikin Hukumar Gudanarwar Hukumar Kula da Yankin Neja Delta. Ita ce hukumar da aka fi narka wa makudan kudade a kasar nan.

4. AFAM NWAGBOSO: DARAKTAN ’YAN WASOSO

– Shi ne Daraktan Kula da Kudade, kuma duk kudaden da Nwagboso ya karba da sunan ajiye wa kamfani a bankin Continental Marchant Bank, babu su, babu dalilin batan su, kuma shi ma bankin ya mutu ya bar baya da kura.

5. OLU BAJOWA da ALABO GRAHAM-DOUGLAS

– Bajowa tsohon Manjo Janar ne, wanda bayan ya yi ritaya sai aka nada shi shugabancin Nigeria Airways tsakanin 1988 zuwa 1990.

– Ya bai wa wani ‘travel agency’ mai suna CES Travels ikon saida dukkan tikitin zirga-zirga daga Najeriya zuwa Amurka da kuma zuwa Ingila, har da zuwa da komowa duka.

– Cinikin da aka yin a miliyoyin daloli, kwatankwacin naira bilyan 2.6 a yanzu, duk an yi musu hadiyar kafino, domin ko sisi ba a saka aljihun gwamnati ba. Bajowa mai makogaron hadiyar daloli.

6. MOHAMMED KARI: KARI KU NE BUHARI
*An samu Kari da laifin cewa a 1993 lokacin ya na shugabancin Nicon Insurance ya hada baki da Nigeria Airways aka karkatar da dala milyan 13.9, kwatankwacin naira bilyan 50.82 a yanzu.
*Wannan Kari din dai ne Buhari ya nada shugaban kamfanin Insura na Kasa, NAICOM a cikin 2015, tun a farkon hawan sa shugabancin kasa.

PREMIUM TIMES ta nemi jin ta bakin Kari, dangane da inda aka kwana a kan zargin batan wadancan kudaden amma bai maida amsa ba. An yi masa tambayar ce ta hannun kakakin yada labaran hukumar, Rasaq Salami.

Sauran wadanda aka kira kananan berayen da suka jidi kudaden sun hada da:
7. Ibrahim Bala

8. All-Well Brown

9. Alexandra Howden

10. A. Olafisoye

Tags: AbujaBuhariFasinjojiHausaJojiNajeriyaNigeria AirwaysPREMIUM TIMES
Previous Post

Buhari ya mika Ta’aziyyar sa ga Iyalan Marigayi Tony Anenih

Next Post

RA’AYINMU: Tilas Buhari ya kawo karshen sa-toka-katsi a Hukumar NHIS

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Buhari Sitting

RA’AYINMU: Tilas Buhari ya kawo karshen sa-toka-katsi a Hukumar NHIS

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Dikko Radda zai saka tsarin TSA a duka harkokin shige da ficen kudaden jihar Katsina
  • Dalilin da ya sa na canja sunan titin Raba zuwa titin ‘Nasir El-Rufai – Gwamna Uba Sani
  • KOKAWAR ƘWACE KUJERAR TINUBU: Kotu ta karɓi kwafen takardun zargin Asiwaju ya yi harƙallar muggan ƙwayoyi
  • SIYASAR KANO: Gwamna Abba ya soke naɗe-naɗe, ya ƙwace filaye da kadarorin da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki
  • Abubuwa 12 Da Suka Hana A Ga Ƙoƙarin Mulkin Buhari

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.