A yau Lahadi ne za a yi zaben fidda gwani na Jam’iyyar PDP a jihar Kaduna.
Wannan zabe dai kowa ya maida hankali a kai domin kuwa kusan duk manyan ‘yan siyasan Kaduna suna neman jam’iyyar ta tsaida dayan su ne dan takarar gwamnan jihar.
Cikin wadanda ake wa ganin sune kan gaba a cikin ‘yan takaran sun hada da tsohon dan majalisa Isah Ashiru wanda a zuwa yanzu an shaida mana cewa ‘yan takara uku sun janye wa.
Bayan shi akwai tsohon gwamna Ramalan Yero, Sanata Sule Hunkuyi da tsohon shugaban hukumar NEMA, Sani Sidi.
Discussion about this post