TAMBAYA: A bani gajeruwar tarihin mutumin nan da yayi tafiya da Annabi Musa a suratul Kahfi, Annabi ne? Tare da Imam Bello Mai-Iyali
AMSA: Alhamdu lillah, Tsira da Amincin Allah su tabbata ga shugabanmu Annabi Muhammad SAW.
Khidir shine mutum da yayi tafiya da annabi Musa Alaihis-Salam Allah ta’ala ya ambaci kissarsa a suratul kahfi cikin Al’kur’ani, amma ba a ambaci sunansa ba, kuma yadda addinin Kiristanci da Yahudanci sun rubuta kissassa.
An samu sabani mai yawa da ruwayoyi daban-daban a tarihinsa. Tarihin da malaman Musulunci suka ruwaito ya saba da na sauran marubuta tarihi. Suma malaman musulunci sun samu sabani a cikin wasu abubuwa.
Wannan bawan Allah shi ne Halliru dan Adamu a hausance, a larabce kuwa ana kiransa da Khidir Ibn Adam Alaihis-Salam. Shi da ne na cikin Adamu da Hauwa’u, Allah yayi masa tsawon rai albakacin addu’ar babanmu Annabi Adamu Alaihis-Salam. Sakamakon wasicin da Annabi Adamu Alaihis-Salam ya yi wa ‘ya’yansa cewa idan ruwan dufana ya zo, su cire gawarsa su rufeshi a wani guri na musamman, kuma ya yi addu’ar tsawon rai ga wanda ya cika wannan Wasici. An ruwaito cewa Khadir ne ya cika wannan umurni na Annabi Adamu Alaihis-Salam.
Duk dacewa wasu malamai suna cewa ya mutu, amma fa wasu ruwayoyi daga wasu manyan malamai suna tabbatar da cewa yana da rai har gobe, kuma ba zai mutu ba sai karshen duniya.
Malamai sun yi sabani akan cewa, shin annabi ne shi ko waliyyi ne daga cikin bayin Allah Salihai? Khidir Annabi ne daga cikin annabawan Allah, ta dalilin fadin Allah a cikin suratul Kahfi, sai Khadir Alaihis-Salam ya cewa Annabi Musa Alaihis-Salam: duk abinda ka gani na ilimi da ban mamaki ba nayi bane da umurnin kaina ba. Duk wanda Allah ya umurta kai tsayi, to ya zama annabi.
(Allah shi ne mafi sani).
Discussion about this post