• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Peter Obi ya fice daga PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    Yadda sojoji suka cafke gogarman masu garkuwa da mutane da wasu 150 a dazukan Zamfara da Katsina

    Askarawan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 42, sun kama 20 sannan sun ceto mutum 63 da aka yi garkuwa da su – DHQ

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Peter Obi ya fice daga PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    Yadda sojoji suka cafke gogarman masu garkuwa da mutane da wasu 150 a dazukan Zamfara da Katsina

    Askarawan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 42, sun kama 20 sannan sun ceto mutum 63 da aka yi garkuwa da su – DHQ

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Dabbobin Layyah Da Kwanaki Goman Farkon Zul-Hajj, Daga Imam Murtadha Gusau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
July 29, 2020
in Ra'ayi
0
Rams

Rams

Bismillahir Rahmanir Rahim

Bayan haka, yaku bayin Allah! Ku sani, daga cikin muhimman lokuta na yin ibada, masu falala, da Allah Madaukaki ya hore wa bayin sa, akwai kwanaki goma na farkon watan Zul-Hajj – wata na sha biyu na shekarar Musulunci, wadanda Allah Ya fifita su a kan sauran kwanakin shekara.

Ibn Abbas ya ruwaito cewa, Annabi (SAW) ya ce:

“Babu wani aiki da yafi alheri irin wanda aka yi a kwanaki goma na farkon Zul-Hajj.” Sai wadansu Sahabbai suka ce: “Koda jihadi a tafarkin Allah?” Annabi (SAW) ya ce: “Koda jihadi a tafarkin Allah, sai dai in mutum ya tafi da kansa da dukiyarsa bai dawo da komai ba.” [Buhari]

Wadannan kwanaki goma manya ne kuma mafiya soyuwa ne a wurin Allah. Ibn Umar (RA) ya ruwaito cewa, Annabi (SAW) ya ce:

“Babu wasu ranaku da suke da girma kuma suka fi soyuwa a wurin Allah fiye da wadannan kwanaki goma na farko Zul-Hajj, don haka ku yawaita tahlili da takbiri da tahmidi a cikinsu” [Musnad Imam Ahmad, kuma Sheikh Ahmad Shakir ya inganta shi]

Daga cikin darajojin da wadannan kwanaki goma suke da su akwai cewa:

1- Allah Yana yin rantsuwa da wani abu domin Ya nuna muhimmancinsa, kuma Allah Ya yi rantsuwa da wadannan ranaku goma a cikin Alkur’ani Mai girma inda ya ce:

“Ina rantsuwa da alfijiri. Da darare goma.” [Al-kur’ani, 89:1-2]

Malamai magabata da suka hada da Ibn Abbas (RA) sun ce wadannan darare goma da aka ambata a cikin Alkur’ani su ne darare goma na farkon Zul-Hajj.

2- Annabi (SAW) ya ce wadannan darare goma sune ranaku mafiya alheri na shekara, kamar yadda muka ambata a Hadisi na baya.

3- Su ne ranaku mafiya alheri na yawaita ambaton Allah, kamar yadda Hadisin da ya gabata ya nuna.

4- Sun kunshi ranar Arfa (9 ga Zul-Hajj) wanda a cikinta ne Allah Ya cika wannan addini. Kuma yin azumi a cikin wadannan ranaku yana kankare kananan zunuban shekarar da ta gabata da shekarar da ake ciki, (manyan zunubai suna bukatar tuba da mayar da hakki ga mai shi).

5- Sun kunshi ranar “Hajji Mafi girma” wato ranar Idin Layya (10 ga Zul-Hajj), kuma wannan rana ita ce rana mafi girma a daukacin shekara.

Don haka ku yawaita karatun Alkur’ani a cikinsu, kuyi sallolin nafilah da kiyamul Laili da sadaka da yada ilimi da tuba ga Allah. Ku yawaita neman gafara ta fadin Astagfirullah, kuyi azumi da jikinku, ma’ana ku kaurace wa haram ko fadin haram ko sauraren haram da sauransu. Kuma ku yawaita yin addu’o’in alheri da zaman lafiya ga kasar mu Najeriya, da al’ummar Musulmin Najeriya, da al’ummar Musulmin duniya baki daya.

Imam Murtada Gusau

Yaku ‘yan uwa na maza da mata! Lallai ku yi gaggawar ribatar wadannan ranaku kafin lokaci ya kure muku.

Yaku bayin Allah! Ku sani, a yau, babu wani aikin da yafi hada dukan Musulmi, matasa da dattawa, maza da mata, bakake da farare, kuma yake kawo farin ciki a fuskar kowa, kamar ibadar Layyah. Layyah ibada ce ta sadaukarwa, ta hanyar yanka dabbobi domin neman yardar Allah. Ana yin ta ne domin tunawa da wani muhimmin abin tarihi da ya auku a lokacin da Allah Ya umarci Sayyidina Ibrahim (AS) ya yi layyah da dansa Sayyidina Isma’il (AS). A lokacin da yake shirin aiwatar da umarnin Allah, sai Allah Ya musanya masa da rago, ya canji Annabi Isma’il da shi, wanda Sayyidina Ibrahim (AS) ya yanka.

Sayyidina Ibrahim (AS), ya ci jarrabawa, domin ya shirya don ya yanka dansa saboda bin umarnin Allah. Yaku Abokaina masu girma, yanzu kuna jin wahala ku yi layyah da dabba (ta amfani da kudinku) don bin umarnin Allah? Bai kamata ni da ku mu kasa cin wannan jarrabawa ba. duk wanda yake da hali yayi layyah, a madadin sa da iyalinsa.

’Yaku ‘yan uwana maza da mata! Ku sani, za’a iya yanka Layyah a kowane lokaci bayan Sallar Idi har zuwa faduwar rana ta uku a bayan ranar Idin. Wannan na nufin wuni hudu (wunin Idi da karin wuni uku na ayyamut-tashriq). Kamar yadda Imamu Shafi’i ya nuna. Amma a fahimtar sauran manyan malamai: Abu Hanifah da Malik da Ahmad, ana yin layyah ce a cikin wuni uku. A fara da ranar Idi a kare a wuni na biyu bayan wunin Idi lokacin faduwar rana.

Ana iya yanka Layyah da rana ko da dare, matukar dai a cikin wadannan ranaku ne, amma yin ta da wuri (jim kadan bayan Sallar Idi) ya fi.

Sunnar Layyah ita ce a raba naman uku, kuma ba tilas ba ne a raba daidai-wa-daida. daya a raba wa talakawa da mabukata, dayan a bar wa iyali da makwabta da dangi da abokai, dayan kuma ka yi yadda ka so da shi.

Layyah Sunnah ce mai karfi a kan kowane Musulmi mai hali. Wannan shi ne ra’ayin akasarin malamai. Amma a wurin wadansu malaman wajiba ce a kan Musulmin da yake da halin yi. Kuma tana daya daga cikin kyawawan ayyuka a Musulunci kamar yadda A’isha (RA) ta ruwaito daga Annabi (SAW) cewa:

“Dan Adam bai taba yin wani aiki a ranar Layyah da ya fi soyuwa a wurin Allah ba, kamar zubar da jinin dabba (yankan Layyah).”

Kuma galibin malamai sun tafi a kan cewa, yanka Layyah shi yafi alheri a kan yin sadaka da kwatankwacin kudin abin yankar.

Yaku ’yan uwana! Ku sani, ana yin Layyah ne da dabbobin gida wato: shanu da rakuma da tumaki da awaki. Kuma yanka rago/tunkiya da bunsuru/akuya shi yafi a kan sauran dabbobin, saboda Annabi (SAW) bai taba yin Layyah ba face da wadannan dabbobi. Amma ana iya yanka rakuma da shanu lokacin Layyah. Kuma wajibi ne abin yankan ya kasance lafiyayye, kosasshe da za’a iya cin naman sa a matsayin ibada ga Allah kamar yadda Allah Ya ce:

“Kuma wanda ya girmama ibadojin Allah, to lallai ne ita (girmamawar) tana daga ayyukan zukata na takawa.” [Al-kur’ani,22:32]

Don haka dabbobi marasa lafiya ko masu aibu basu yin layyah.

Kuma wajibi ne idan rago ne ko tunkiya su haura wata shida kamar yadda Ibn Majah ya ruwaito cewa, sai Jaza’a za’a yi Layyah da ita. Ga jinsin akuya kuwa wajibi ne ya kai shekara daya. Sannan saniya shekara biyu, shi kuma rakumi shekara biyar.

Kuma kada a yi Layyah da nakasasshiyar dabba, kamar mai ido daya ko marar lafiya ko gurguwa da hakan ya bayyana ko ramammiya marar nama kamar yadda Buhari ya ruwaito daga Barra’u Bin Azib daga Annabi (SAW).

Kuma mafi yawan malamai sun tafi a kan cewa siffofi hudu da aka ambata a Hadisin za’a iya amfani dasu wajen hukunci a kan duk wata nakasa. Don haka duk wata nakasa da ta kai ta ko tafi ta ba za’a yi Layyah da dabbar ba, kamar makauniya ko marar kafa daya.
Kuma ana iya Layyah da dabbar da aka dandake, saboda Annabi (SAW) ya yi haka. Haka dabbar da aka haifa ba ta da jela/bindi ko take da rabinta, amma wadda aka yanke jelarta/bindinta duka ba za’a yi Layyah da ita ba.

Sannan tunkiya ko akuya daya ta wadatar mai gida yayi Layyah da ita ga kansa da iyalansa. Kuma ya halatta mutum bakwai su yanka saniya ko rakumi daya a matsayin layyarsu. Kamar yadda Jabir Bin Abdullahi (RA) ya ruwaito cewa Annabi (SAW) ya yi haka a shekarar Sulhun Hudaibiyyah. [Muslim]

Kuma mai yin haka zai iya hadawa da iyalinsa a cikin ladan domin a nan daidai yake da mai yanka tunkiya ko akuya.

Kuma bai halatta a yanka Layyah kafin yin Sallar Idi ba, duk wanda ya yanka layyah kafin Idi ya yanka wa iyalinsa nama sun ci ne kawai amma bai yi Layyah ba, kamar yadda Annabi (SAW) ya nuna. Kuma idan mutum zai yanka layyar ya ambaci sunan Allah, ya ce:

“Bismillah, Ya Allah, wannan daga rahamarKa ce kuma dominKa ne.”

An fi so mutum ya yanka Layyarsa da kansa, idan ba zai iya yin haka ba, to ya halarci yankan, sannan ya raba naman uku kamar yadda muka ambata a baya. Ya ci rubu’i daya shi da iyalinsa, ya bayar da daya rub’in sadaka, dayan kuma ya yi kyauta da shi, kamar yadda Annabi (SAW) ya shaida wa ’yarsa Fatima (RA) cewa:

“Ki kasance a lokacin da ake yanka Layyarki. Allah Yana gafarta miki a lokacin digar farko na jininta.” [Baihaki da Abdul Razzak]

Hikimar shar’anta yin Layyah:

1 – Neman kusanci ga Allah ta hanyarta.

2 – Raya Sunnar Shugaban Masu Tauhidi Annabi Ibrahim (AS) wanda Allah Ya umarce shi yayi Layyah da dansa Annabi Isma’il (AS) sannan daga baya ya musanya shi da rago, Annabi Ibrahim (AS) ya yanka shi a madadin Annabi Isma’il (AS) din.

3 – Yalwatawa da kyautata wa iyali a ranar Idi.

4 – Fadada jin dadi a tsakanin matalauta da mabukata ta hanyar ba su sadakar naman Layyah.

5 – Yin godiya ga Allah kan yadda ya hore mana duka dabbobin ni’ima (Bahimatil An’am).

Abubuwan da wanda yayi niyyar Layyah zai guje musu:

Idan mutum yayi niyyar zai yi Layyah to da zarar watan Zul-Hajj ya kama, ba zai yi aski ko ya yanke farce/kumba/akaifa ba har sai ya yanka abin Layyarsa. Muslim ya ruwaito a cikin Sahihinsa cewa Ummu Salmah (RA) cewa, Annabi (SAW) yace:

“Idan kuka ga jinjirin watan Zul-Hajj kuma dayanku yana da niyyar yin Layyah, to kada ya aske gashinsa ko ya yanke farcensa.” [Muslim]

Haka kada a biya ladan mai gyara naman Layyah daga abin Layyar. Domin Aliyu Bin Abi Talib (RA) ya ce:

“Manzon Allah (SAW) ya umarce ni da in lura da Layyar wani rakumi, in bayar da namansa da fatarsa a matsayin sadaka, kuma kada in bayar da komai daga cikinta ga mahauci a matsayin ladan aikinsa. Ya ce, “Zan iya ba shi wani abu daga abin da na mallaka.” [Muslim]

Yaku ‘yan uwana maza da mata! Ina rokon Allah Madaukaki ya amsa min da kuma ku da sauran Musulmin duniya baki daya, kuma Yasa dominSa kadai muke yi. Tsira da amincin Allah su kara tabbata ga Annabi Muhammad (SAW) da iyalansa da Sahabbansa. Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai.

Ya Allah! Ka taimake mu wajen rayuwa bisa koyarwar Alkur’ani da Sunnah. Ya Allah Ka nuna mana gaskiya kuma Ka bamu ikon bin ta, kuma Ka nuna mana karya Ka bamu ikon guje mata.

Ya Allah! Ka shiryar da mu, Ka kare mu daga ayyukan jahilci da barna. Ka kare mu daga gazawarmu. Ka sanya karshen ayyukanmu su kasance mafi alherinsu da dacewarsu. Kuma Ka gafarta mana Ya Ubangiji.

Yaku ’yan uwana! Ku sani, duk abin da na fada mai kyau a wannan jawabi na yau, daga Allah Madaukaki ne, kuma duk wani kuskure daga gare ni ne, kuma ina neman tsarin Allah daga bayar da muguwar shawara da dukkan barna da fitina. Kuma ina rokon Allah gafara idan na ketare iyaka a cikin duk abin da na ce ko na aikata.

Godiya ta tabbata ga Allah, Tsira da amincin Allah su kara tabbata ga Manzon Allah da alayensa da Sahabbansa.

Ina mai kammala wannan jawabi nawa, ina mai rokon Allah Madaukaki Ya gafarta mana zunubanmu. Ku nemi gafararSa, Lallai Shi Mai gafara ne Mai jin kai.

Imam Murtadha Muhammad Gusau, Babban Limamin Masallacin Juma’ah na Nagazi-Uvete, da Masallacin marigayi Alhaji Abdurrahman Okene, da suke Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za a iya tuntubar sa ta lambar tarho kamar haka: +2348038289761 ko email: gusaumurtada@gmail.

Tags: AbujaEidHausaKabirKiaymul LailLabaraiLayyahPREMIUM TIMESSallahZul-Hajj
Previous Post

An ceto mutane bakwai daga hannun mai safarar mutane a kan iyakar Katsina

Next Post

Ambaliya ta ci gidaje 50 a Kebbi – Jami’in gwamnati

Next Post
Flood

Ambaliya ta ci gidaje 50 a Kebbi – Jami’in gwamnati

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Peter Obi ya fice daga PDP
  • Ba mu yadda mu janye wa mutum ɗaya ba, a shiga filin daga a fafata kawai – Ƴan takarar gwamnan Jigawa
  • AN YANKA TA TASHI: A biya ni naira miliyan 21 kuɗin fom ɗin takarar gwamna da na siya a PDP – Ɗan takarar gwamna
  • ZARGIN ƘARFA-ƘARFA A SIYASAR ENUGU: Sanata Ekweremadu ya saka takalmin ficewa daga PDP zuwa APC
  • TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.