Shugaban kungiyar likitocin Najeriya (NMA) Francis Faduyile ya yi kira ga ‘yan siyasar kasar nan da su tsuke bakunan su wajen fadin kalaman da zai iya tada zaune tsaye a kasar nan.
Faduyile ya yi wannan kira ne ranar Juma’a inda ya bayyana cewa fadin munanan kalamai musamman a wannan lokaci da zaben 2019 ya kunno kai zai iya yi wa kasa illa matuka.
” Najeriya za ta iya fadawa cikin halin rashin zaman lafiya a dalilin irin wadannan kalamai sannan abin takaici shine talakawa musamman mata da yara ne za su fi fadawa cikin matsala.
” Kuma fannin kiwon lafiya ma za ta fada cikin irin wannan matsala.
Kungiyar ta yi kira ga ‘yan Najeriya musamman matasa da su zama ma su yin biyayya ga doka.
Discussion about this post