• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

APC: Gwanon da ba ya jin warin jikin sa

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
April 6, 2018
in Ra'ayi
0
APC: Gwanon da ba ya jin warin jikin sa

APC Map

Tun bayan da Gwamnatin Tarayya a ta bakin Ministan Yada Labaran ta, Lai Mohammed, ya fara fitar da jerin sunayen wadanda ake zargin sun wawuri kudade a zamanin gwamnatin tsohon Shugaban Kasa, Goodluck Jonathan, ’yan Najeriya sun rika tofa albarkacin bakin su. Yayin da wasu magoya bayan gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ke murna da ganin jerin sunayen, wasu kuma cewa suke yi ai tuni ake yi musu irin wannan tatsuniyar.

Akwai kuma masu cewa su ba su ga dalilin fitar da sunayen ba, domin an saba jin wannan zance, kuma dama ai ita APC, tun ma kafin ta hau gwamnati ta ce ta san an tafka barna, don haka ta zo ne don ta yi gyara.

Da dama na korafi kan APC cewa maimakon gwamnati Buhari ta dukufa ta na gyara, kullum sai bada labarin barnar baya ta ke yi. Wasu na ganin cewa ai babu narabar dambe da fada idan ana maganar PDP da APC ne.
A Abuja da kewaye ba z aka san ana siyasa ba sai idan ka ga matasa sanye da jar hula, wadda ke tabbatar maka da cewa mabiyar darikar Gidan Kwankwasiyya ne.

Amma a ranar Asabar da ta gabata, na je hutun-ganin-gida a Kano. Tun ban kai ga warwarewa daga gajiyar tuki da bugun ramuka daga Abuja zuwa Kano ba, na fahimci lallai siyasar Kano na ci gaba da zafi, musamman irin yadda na rika jin ra’ayoyin jama’a dangane da jerin sunayen da Gwamnatin APC ta fitar na wadanda ta ce su ne suka sace dukiyar al’umma a zamanin mulkin PDP a karkashin Goodluck Jonathan.

NI DA MAKWABCI NA

Aliyu Nasiru mazunin unguwar Karkasara a Kano, kuma ba shi da nisa da gida na. Na zo wucewa sai na iske sun rukume da gardama, inda shi ya ke cewa, “ya kamata fa kowa ya fahimci cewa APC gwano ce, wanda ba ya jin warin jikin sa, sai warin jikin PDP kawai ta ke ji.

“Idan ba haka ba, ka duba ka gani, ita APC a yanzu ta na ta ba mu labarin satar da aka yi lokacin gwamnatin Jonathan. Amma kuma wadanda suka wawure kudaden kasar nan da tuni EFCC na shari’a da su, duk su na cikin APC, da su ta kafa gwamnati.

‘‘Ina irin su Danjuma Goje? Ina Saminu Turaki da ake neman naira biliyan 40 a hannun sa? Su da sauran gaggan PDP na gwamnatin Obasanjo da ta Umaru ‘Yar’Adua duk fa su na cikin jam’iyyar APC.

TSAKANIN LABARAN DA CHIDOZIE

Na shiga Kasuwar Sabongari domin sayen wasu ‘yan kayan amfani a gida. A kusa da kantin da na ke sayen kaya, makwabcin mai kantin, Chidozie Obinna, mai sayar da kayan shafe-shafe a cikin Kasuwar Sabon gari, Kano, ya rika kushe sunayen yayin da Alhaji Labaran wanda na je wurin sa ke kare gwamnati. Chidozie cewa ya yi, shi fa duk wani abin da gwamnatin APC za ta fada, jin sa kawai ya ke yi, amma kame-kame kawai su ke yi.

“Mun ji an saci kudi a lokacin Jonathan. Abin da mu ke nema ga wannan gwamnatin shi ne ta bayyana mana nawa ta kwato, kuma wadanne ayyuka aka yi da kudaden? Ko su daure wadanda su ka kama, ko kada su daure su, wannan kuma ruwan gwamnatin, tunda dama idan ka duba, za ka ga da PDP da APC,su ya su duk daga ‘yan uwa sai ‘yan gari daya sai kuma surukai da abokanai da ‘ya’yan dangi.

“A kullum cikin kasuwar nan ba ka jin komai sai gardamar siyasa, musamman idan ana rashin ciniki kowa ba shi da aikin yi. To na yi nazari, a lokacin da Jonathan ke mulki, har ya sauka sabulun Tura guda daya bai kai naira 300 ba. Amma a yau, idan ka bude super market, sai ka sayar da sabulu daya tal naira 800 sannan za ka iya cin ribar naira 50. To me wani zai zo a yanzu kuma ya gaya min har na tsaya na saurare shi?

Da yawan wadanda na rika ji suna bobbotai, sun nuna cewa ya kamata Lai Mohammmed ya lissafa manyan ‘yan PDP da suka koma APC aka kafa mulki da su, kuma suka rika babbaka gobarar kisan makudan kudade ga APC a lokacin kamfen.
Wasu kuma na yin korafin cewa dukkan gwamnoni da tsoffin sanatoci da gwamnonin baya, sun rika kashe wa APC kudade, alhali kuma kowanen su ba saye da sayarwa ya ke yi ba, a hantsar gwamnati ya ke tatsa, su sha kuma su yi wa jam’iyya hidima da kudaden.

NI DA ABOKI NA A TITIN ZOO ROAD, KANO

A kan titin Zoo Road kuma na tsaya sayen doya, na ci karo da wani da muka dade ba mu hadu da juna ba. Bayan mun gaisa, sai na tambaye shi labarin gari. Maimakon ya amsa min, sai ya far aba ni labarin matsalar gari. “Ce mana su ka yi idan Buhari ya hau zai dawo da dalar Amurka daidai da naira. Haka Buharin kan sa ya fada, kuma kowa ya sha ji. Amma ga shi har sun fara kamfen na tazarce a fakaice, har yanzu dala daya tal ta na daidai da naira 360.

“A haka kuma wai wani dan boko zai rika ce mana wai wannan gwamnati na gina tattalin arziki. Ta ina zai ginu dala ta yi wa naira fintinkau? Inji Safiyanu Yusuf, wanda tun da ya rasa aikin sa a kamfanin S.A.L shekaru hudu baya, har yau bai sake samun wani aiki ba.

Ba ‘yan adawa kadai ke sukar gwamnatin Muhammadu Buhari ba, da dama daga cikin wadanda suka sha wahala akan gwamnatin aka watsar da su na kan ra’ayin cewa idan ma mutum na kallon ba a tafka sata a karkashin wannan gwamnatin, to ya na yaudarar kan sa ne.

NI DA LAWAL KASUWAR WAMBAI

“Ai ga wadanda aka bai wa mukamai nan mu na ganin daga masu gina gidaje sai masu kara aure. Kuma kudaden da suke kashewa a wurin auren kadai, idan ka yi nazari sai ka ga ba su taba ko ganin kwatankwacin su ba, sai dai a hoto kawai.” Inji Lawal Bashir, wani dan kasuwa mai sayar da bulawus a Kasuwar Kofar Wambai, wanda ya gayyace ni daurin aure gidan sa, amma na kira shin a ba shi hakurin rashin halartar da ban yi ba, daga nan kuma mu ka goce hirar al’amarin kasa.

“Ni matsala ta da APC shi ne, duk kuskuren su, ba su karbar gyara. Amma kuma duk alherin gwamnatin baya to ba su yarda alheri ba ne. Yanzu dubi yadda gwamnatin Jonathan ta gina jami’o’i na tarayya har 13, kuma wasu gwamnatocin jihohi na PDP kamar Katsina, Kano, Jigawa, Gombe, Kaduna da sauran su duk suka kafa jami’o’i. Don Allah da a ce babu wadannan makarantu a yanzu, da me ka ke tsammani wajen yawan masu zaman-dirshan a gida a bangaren yaran mu masu gama jami’a? Inji Alhaji Abubakar Jibrin, wani telan da ke dumka kayan mata da na yara. Shi kuma biyo ni yay i har jikin mota mu na hirar matsalolin kasar nan tare da shi, a lokacin da na je wurin sa zan karbo dinkin yara.

MAI WANKIN MOTA YA HAU NI DA FADA

Wani magidanci mai wanke motoci a Na’ibawa mai suna Mohammed Ali. Ya hau ni da fada a lokacin da ya ke wanke min mota, a lokaci daya kuma mu na hirar duniya da shi: “Kai fa dan jarida ka zo ka tambaye ni ne don ka ji ina yabon Buhari ko? To ai ni yanzu na daina yin komai a duhu. Saboda dai na duba a Kano na ga ba mu iya siyasa ba. Kullum mu dai Buhari, Buhari, Buhari. To don Allah me ya yi mana?

“Mu ke nan kullum zagin Janar Babangida, amma duk wani abin kirki idan ka duba, in banda na zamanin audu Bako, to duk aikin gwamnatin tarayya ne a zamanin Babangida.”

“Buharin nan fa tun da ya hau mulki bai kara zuwa Kano a mota ba. Bai san yadda titin Zariya zuwa Kano ya lalace ba, kuma bai san yadda na Funtuwa zuwa Kano ya lalace ba. Sau daya ya zo Kano, shi ma sai da muka yi masa gori. Sauran zuwan biyu da ya yi kuwa duk daurin auren manya ne ya kawo shi, bai zo don abin da ya shafe mu ba. To don me zan yi ta bata lokaci na a kan sa?

Wani mai goyon bayan jam’iyyar PDP, mai suna Aliyu kuwa, ce min ya yi, ya yarda an yi barna a zamanin PDP. Amma da yawan wadanda suka yi barna a yanzu sun shige cikin APC, an daina ganin laifin su.

“Ina tabbatar muka duk ranar da muka kayar da APC, za ku rika jin tabargazar da za a rika fallasawa gwamnatin ta yi. Nan fa kiri-kiri a bainar jama’a Buhari ya ce Abacha ba barawo ba ne. Amma ga shi sai dawo wa gwamnati da kudaden da Abacha ya wawura ake yi. Kai ka san Buhari na da matsala.

“PDP dai aka raina, su kuma gwamnonin APC na yanzu da Buhari ya rika gabza wa kudade domin su biya albashi, da yawan su sun ki biya, amma ya zuba musu idanu. Kuma bai ce musu ku dawo da kudaden da na ba ku ba. Wai wannan mutumin ne zai dame mu da labarin abin da aka yi lokacin PDP. To shin a na sa lokacin kuma fa?”

A gaba na a ranar Lahadi, bayan an daura aure a wani kofar gida a Bachirawa, kusa da Ramin Tifa, kofar gidan Danlami Rawayau, Kano, gardamar siyasa ta rukume a kan sunayen wadanda ake zargin sun wawuri dukiya.

GARDAMA A WURIN DAURIN AURE

Wani Alhaji Mansir na hakikicewa ya na kare PDP. “Yanzu dai a kasar nan duk shedancin ka idan ka na APC, to kai waliyyi ne. Sun ki yarda Rotimi Ameachi ya yi barna a jihar Rivers, kuma ba su yarda tsohon gwamnan Ekiti, Kayode Fayemi ya yi barna a jihar Ekiti ba. Shi ne ma Ministan Karafa a yanzu, kuma ya kusa ajiye mukamin minista ya sake neman takarar gwamnan. Amma da ya ke APC ba su son Saraki, shi kadai ne mabarnaci.

“Ai dama wannan halayya gado su ka yi wajen Buhari. Shi ne ya ce ya yi bincike Babachir Lawal bai ci kudin yi wa ciyawa fitiki ba, sai da majalisa ta tabbatar masa cewa kumbiya-kumbiya ya ke yi, sannan ya yi shiru.

Kada ku manta, Buhari ya taba cewa Audu Ogbe barawo ne, domin ya daure shi a lokacin da ya yi mulkin soja, aka yi masa daurin sama da shekaru 30. Babangida ne ya fito da shi. Amma yanzu Buhari ya nada shi ministan gona a gwamnatin sa.”

Tags: APCGoodluck JonathanKanoMuhammadu BuhariShugaban KasasiyasaTuraki
Previous Post

Mata masu ciki sun yi zanga-zangar tsawwala kudin haihuwa

Next Post

An kara wa sojoji 3,729 da ke yaki da Boko Haram mukami

Next Post
Soldiers

An kara wa sojoji 3,729 da ke yaki da Boko Haram mukami

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • RIKICIN PDP: Kwamitin Amintattun PDP ya tura wa Wike tawagar lallashi
  • KADUNA 2023: Uba Sani ya zaɓi Hadiza Balarabe mataimakiyar sa
  • ‘Yan bindiga sun kashe Sojoji 30, ‘yan sanda 10 da farin hula 12 a makon jiya
  • Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki
  • MAIDA HANNUN AGOGO BAYA: ‘Yan-ta-kife sun banka wa ofishin INEC wuta a Enugu

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.