Gwamnan Jihar Barno, Kashim Shettima ya tabbatar da cewa Boko Haram sun kashe masunta 31 a Baga, cikin Karamar Hukumar Kukawa, a Jihar Barno.
Kamfanin Dillancin Labarai, NAN, ya ruwaito cewa gwamnan ya bayyana haka, a ranar Talata a yayin rabon abincin agaji wanda Kungiyar ECOWAS ta kasashen Afrika ta Yamma ta taimaka wa ‘yan gudun hijira a sansanonin su, a Maiduguri.
Ya ce harin na tabbatar da cewa har yanzu dai Boko Haram na nan su na kaddamar da munanan hara-hare, su na karkashe mutane a yankin Tafkin Chadi.
Shettima ya ce har yanzu jami’an sojoji da sauran jami’an tsaro ba su kai ga tantance rahoton ba.
” Wani ya kira ni da safiyar nan, ya shaida min cewa Boko Haram sun kashe masunta 31 a Tafkin Chadi.
” Su kuma jami’an tsaro ba su kai ga tabbatar da rahoton ba, don haka mu na jiran su tabbatar da hakan.
” Hakan na nuni da irin mummunan rikicin da mu ke fuskanta a Barno, inda masu karyar Jihadi ke ci gaba kashe mutane a Tafkin Chadi.
Shettima ya jinjina wa irin kokarin da jami’an tsaron sojoji ke yi wajen kokarin kawo karshen ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas.
Kamfanin Dillancin Labarai dai ya ruwaito cewa an kashe masunta 31 a Tafkin Chadi, a ranakun 5 da 6 Ga Agusta, 2017.
Wata lambar waya, mallakar wani dan CJTF, ya kira da boyayyen suna cewa an kashe masunta 14 a Duguri, 17 kuma a Dabar-Wanzam.
Discussion about this post