Amurka ta bayyana cewa ta na goyon bayan dukkan matakan da ECOWAS ta ɗauka da wanda za ta ɗauka nan gaba kan mahukuntan sojojin juyin mulkin Nijar.
Ta ƙara da cewa kada mahukuntan sojoji su kuskura su bari wani abu ya taɓa rayuka da lafiyar Shugaban Ƙasar Nijar na dimokraɗiyya, Mohammed Bazoum da iyalin sa da sauran jiga-jigan gwamnatin sa waɗanda ke tsare.
“Amurka ta bi sahun ECOWAS wajen kira da a gaggauta komawa kan turbar dimokraɗiyya a Nijar”, haka Sakataren Harkokin Waje na Amurka, Antony Blinken ya bayyana.
Kwanan nan Amirka ta dakatar da wani tallafin da ta ke bai wa Nijar, bayan sojoji sun ƙwace mulki a ƙasar.
A ranar Alhamis ce kuma ECOWAS ta ce dakarun ta su fara shirye-shiryen ko-ta-kwanan yaƙi da Nijar.
Ta ce ta na so a sulhunta da lalama, amma kuma ba ta fidda ran za a gwabza yaƙi ba.
Blinken ya ce Amurka na so a sulhunta cikin ruwan-sanyi.
Ana zaman ɗarɗar a Nijar, ƙasa mai arzikin sinadaran yuraniyan. Kafin juyin mulki dai Nijar na da kyakkyawar alaƙa da Turawan Yamma, a yaƙi da ta’addanci a yankin Sahel.
Discussion about this post