• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Abdulrasheed Bawa ya farfado kuma yana nan cikin koshin lafiya – Hukumar EFCC

    Kotu ta bada umarnin a garƙame Shugaban EFCC, Bawa a kurkuku

    Ɗan gidogar kwangila ya yi barazanar kashe wakilin PREMIUM TIMES, saboda ya  fallasa amaja a gine-ginen da ya yi wa gwamnati

    HATTARA MASOYA: Ƴan sanda sun cafke matashin da ya ɗirka wa saurayin ƙanwarsa bindiga saboda ya raba su sun ki

    ƊAN TAKARA MUSULMI, MATAIMAKI MUSULMI: Ka iya wa bakin ka tunda wuri- Gargaɗin Ganduje ga Babachir

    ƘAƘUDUBAR CANJIN KUƊI: Emefiele ya ƙirƙiro wannan jangwangwama saboda haushin bai samu takarar shugaban ƙasa a APC ba – Ganduje

    Amurka ba ta hana Tinubu shiga ƙasar ba, zai bi ta Landan ya zarce can ƙasar – Orji Kalu

    TINUBU A KAN SIKELIN 2023: Kada fa Asiwaju ya yi riginginen kunkuru a kan hanyar shiga Villa

    Ni da kai na zan zaɓi wanda zai gaje ni, goyon bayan ku kawai nake bukata – Buhari ga Gwamnoni

    BAYANIN BUHARI GA GUNGUN GWAMNONIN APC: ‘Ba zan yi wa zaɓen 2023 katsalandan ba’

    Jami’ar Al-Qalam na bin gwamnatin Kano bashin Naira miliyan 38 kuɗin karatun dalibai ƴan asalin jihar

    Jami’ar Al-Qalam na bin gwamnatin Kano bashin Naira miliyan 38 kuɗin karatun dalibai ƴan asalin jihar

    An damke faston da ya rika yin lalata da yar’ aikin sa na tsawon shekara biyar a Kaduna

    Kotu ta yanke wa Habila da Joy hukuncin zaman kurkuku bayan kama su da laifin satar N700,000

    court

    Mijin kanwar matata ya gudu ya bar matarsa a kauye cikin wahala babu kula – Mustapha a kotu

    APC ta yi matuƙar murna, jin cewa Buhari zai taya Tinubu kamfen a jihohi 10

    Gazawar gwamnatin Buhari ta su ce can, kada a rika dora wa su Tinubu laifi, babu ruwan su – Tsohon Ministan Buhari

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Abdulrasheed Bawa ya farfado kuma yana nan cikin koshin lafiya – Hukumar EFCC

    Kotu ta bada umarnin a garƙame Shugaban EFCC, Bawa a kurkuku

    Ɗan gidogar kwangila ya yi barazanar kashe wakilin PREMIUM TIMES, saboda ya  fallasa amaja a gine-ginen da ya yi wa gwamnati

    HATTARA MASOYA: Ƴan sanda sun cafke matashin da ya ɗirka wa saurayin ƙanwarsa bindiga saboda ya raba su sun ki

    ƊAN TAKARA MUSULMI, MATAIMAKI MUSULMI: Ka iya wa bakin ka tunda wuri- Gargaɗin Ganduje ga Babachir

    ƘAƘUDUBAR CANJIN KUƊI: Emefiele ya ƙirƙiro wannan jangwangwama saboda haushin bai samu takarar shugaban ƙasa a APC ba – Ganduje

    Amurka ba ta hana Tinubu shiga ƙasar ba, zai bi ta Landan ya zarce can ƙasar – Orji Kalu

    TINUBU A KAN SIKELIN 2023: Kada fa Asiwaju ya yi riginginen kunkuru a kan hanyar shiga Villa

    Ni da kai na zan zaɓi wanda zai gaje ni, goyon bayan ku kawai nake bukata – Buhari ga Gwamnoni

    BAYANIN BUHARI GA GUNGUN GWAMNONIN APC: ‘Ba zan yi wa zaɓen 2023 katsalandan ba’

    Jami’ar Al-Qalam na bin gwamnatin Kano bashin Naira miliyan 38 kuɗin karatun dalibai ƴan asalin jihar

    Jami’ar Al-Qalam na bin gwamnatin Kano bashin Naira miliyan 38 kuɗin karatun dalibai ƴan asalin jihar

    An damke faston da ya rika yin lalata da yar’ aikin sa na tsawon shekara biyar a Kaduna

    Kotu ta yanke wa Habila da Joy hukuncin zaman kurkuku bayan kama su da laifin satar N700,000

    court

    Mijin kanwar matata ya gudu ya bar matarsa a kauye cikin wahala babu kula – Mustapha a kotu

    APC ta yi matuƙar murna, jin cewa Buhari zai taya Tinubu kamfen a jihohi 10

    Gazawar gwamnatin Buhari ta su ce can, kada a rika dora wa su Tinubu laifi, babu ruwan su – Tsohon Ministan Buhari

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Muhimman Wasiyoyin Da Zasu Amfane Mu Duniya Da Lahira, Matukar Munyi Amfani Da Su, Daga Imam Murtadha Gusau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
January 13, 2023
in Ra'ayi
0
Imam Murtada Gusau

Imam Murtada Gusau

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinkai

Assalamu Alaikum

Bayin Allah masu daraja, Annabi (SAW) yace:

“Tilawar Alkur’ani Mai girma da Ambaton Allah haske ne a gare ka a doron ƙasa, kuma taska ne gare ka a sama.” [Sahihut-Targhib]

Imam Ibn Al-Qayyim (Rahimahullah) yace:

“Duk wanda ya dawwama da godiya, to alkhairi zai ta bibiyarsa. Duk wanda ya dawwama da Istighfari za’a buɗe masa abubuwan da suke rufaffu.” [Ad-Da’u Wad-Dawa]

Imam An-nawawiy (Rahimahullah) yace:

“Mustahabbi ne mace ta aske gemu idan ya fito mata.” [Sharhu Sahih Muslim]

Annabi (SAW) yace:

“Ku halarci juma’ah, kuma ku kusanci liman, domin mutum ba zai gushe ba yana jinkirin zuwa juma’ah face anyi masa jinkirin shiga Aljannah.” [Sahihul-Jami’u]

Sheikh Ibn Uthaimin (Rahimahullah) yace:

“Ka kiyaye da yin Sallar asubahi da Sallar la’asar (cikin lokaci kuma cikin jam’i) zaka samu damar kallon fuskar Allah maɗaukaki a Aljannah ta dindindin.” [Sharhu Riyadus-Salihin]

Imam Al-Qurtubi (Rahimahullah) yace:

“Duk wanda ya zauna a majalisin masu aikata saɓon Allah da zunubi da laifi, kuma bai yi masu inkari ko nasiha ba, to yayi tarayya dasu a cikin aikata zunubin da laifin da saɓon.” [Ahkamul-Kur’an]

Imam Ibn Muflih (Rahimahullah) yace:

“Haramun ne Halartar taron sallar mushirkai (waɗanda ba musulmai ba) saboda faɗin Allah (SWT) والّذِينَ لا يشْهَدُون الزُّور.” [Al-Furu’]

Annabi (SAW) yace:

“A ranar juma’ah akwai wata sa’a (wato wani lokaci) da bawa ba zai roki Allah ba face ya amsa masa.” [Bukhari da Muslim]

Annabi (SAW) yace:

“Ku nemi sa’a (wato lokacin amsa addu’a) a ranar juma’ah bayan Sallar la’asar zuwa faɗuwar rana.” [Sahihut-Tirmizi]

Annabi (SAW) yace:

“Duk wanda ya lamunce man, wato ya kiyaye abinda yake tsakanin leɓɓansa (harshen sa) da ƙafafunsa (Al’aurar sa), na lamunce masa Aljannah.” [Sahihul Bukhari]

Imam Ibn Rajab (Rahimahullah) yace:

“Shagaltuwa da tsarkake zuciya, yafi muhimmanci sama da yawan Sallah da yawan azumi amma tare da tsatsar zuciya.” [Lada’ifil Ma’arif]

Imam Malik (Rahimahullah) yace:

“Duk wanda ya mutu akan Sunnah, to albishir a gare shi.” [Siyaru A’lamin-Nubalah]

Sheikh Al-Allamatus-Si’idi (Rahimahullah) yace:

“Alamar dace ga bawa shine ikhlasinsa ga Allah (wato yi domin Allah), da gaggawarsa wurin amfanar bayin Allah da halittun Allah.” [Tafsirus-Sa’adi]

Imam Mujahid Bin Jabr (Rahimahullah) yace:

“Ku riƙi abinda ya bayyana a gare ku (wurin yin hukunci), ku bar abinda ya ɓuya gare ku (kada kubi diddigin abinda ya ɓuya).” [Jami’ul Bayan na ad-Dabari]

Umar (RA) yace:

“Ku nisanci (tarayya da) maƙiyan Allah a idinsu da sallarsu, saboda fushin Allah na sauka akan su (a lokacin).” [Bukhari a cikin At-Tarikh]

Imam Ibn Taimiyyah (Rahimahullah) yace:

“Mumini yana farin ciki da abinda yake faranta wa muminai rai, haka yana baƙin ciki da baƙin cikinsu. Duk wanda baya jin haka, to baya daga cikinsu (muminai).” [Majmu’u Fatawa]

Imam Ibn Al-jawzi (Rahimahullah) yace:

“Duk wanda baya son aikinsa (na kirki) ya tsaya ko ya yanke bayan mutuwarsa, to yayi kokari ya yaɗa ilimi.” [At-Tazkirah]

Annabi (SAW) yace:

“Duk wanda yacewa ƙaramin yaro zo ka karɓa, kuma yaron ya zo amma sai bai bashi komai ba, to ya sani yayi ƙarya.” [As-Sahihah]

Imam Ibn Al-Qayyim (Rahimahullah) yace:

“Lallai duk wanda yake lizimtar aikata zunubi to ya sani cewa zai kai lokacin da zai daina jin daɗin yin zunubin kuma (a jarrabeshi da) kasa daina aikatawa.” [Raudatul-Muhibbin]

Imam Ash-shanqiti (Rahimahullah) yace:

“Ƙarin aure (bisa tsarin ƙa’ida da cika sharuɗɗa) Shari’ah ce ta Allah da Manzonsa (SAW), kuma ba kowa yake sukarsa ba face wanda Allah ya makantar da basirarsa da duhun kafirci (shirka ko son Rai).” [Adwa’ul Bayan]

Imam Az-Zahabiy (Rahimahullah) yace:

“Mafi ilimin fiƙihu a cikin matayen Al’ummar nan baki ɗaya itace A’isha (RA).” [Siyaru A’lamin-Nubala]

Annabi (SAW) yace:

“Duk wanda ya Sallaci Sallar asubahi (a jam’i), to yana ƙarƙashin (kiyayewar) kulawar Allah.” [Sahihu Muslim]

Annabi (SAW) yace:

“Duk wanda ya ganni a mafarki (tare da cika sharuɗɗa), to da sannu zai ganni a farke (a lahira) domin shaiɗan baya ɗaukan kamannina (cikakkun na asali).” [Bukhari]

Imam Ibn Taimiyyah (Rahimahullah) yace:

“Dukkan wanda ya saɓa wa Manzo (SAW), to tanaƙudin sa (harmagagarsa) na kasancewa ne gwargwadon saɓawarsa.” [Bayani Talbisul Jahamiyyah]

Ibn Umar (RA) yace:

“Taƙawa ita ce kada ka kalli kanka a matsayin kafi waninka (daraja da falala a wurin Allah).” [Tafsirul Baghawi]

Imam Mutarraf Bin Abdullah (Rahimahullah) yace:

“Duk wanda yake son sanin matsayinsa a wurin Allah, to ya kalli matsayin Allah a wurinsa.” [Ahmad a cikin Zuhud]

Imam Ibn Al-Qayyim (Rahimahullah) yace:

“Yana daga alamar taɓewa; mantawa da aibin kai, da kutsawa cikin aibin wani.” [Miftahu Daris-Sa’adah]

Imam Wahab Bin Munabbih (Rahimahullah) yace:

“Idan kaji mutum yana yabon ka da abinda baka yi ba, to kada ka amintu da cewa ba zai iya zargin ka da abinda baka yi ba.” [Siyaru A’lamin-Nubalah]

Imam Ibn Qayyim (Rahimahullah) yace:

“Sallar Asubahi ita ce tushe kuma ginshiƙin ayyuka, kuma ita ce farkon sa.” [Zadul Ma’ad]

Annabi (SAW) yace:

“Mafificiyar Sallah a wurin Allah ita ce Sallar asubahi, yinin juma’ah, a cikin jam’i.” [Sahihul Jami’u]

Sheikh Bin Baz (Rahimahullah) yace:

“Wankan juma’ah na Sunnah baya tabbatuwa sai bayan fitowar Alfijir.” [Majmu’u Fatawa]

Imam Ibn Uthaimin (Rahimahullah) yace:

“Lokacin wankan Juma’ah shine bayan fitowar Alfijir ko bayan hudowar rana (yafi) ko lokacin tafiya masallaci (mafifici).” [Liqa Bab Al-maftuh]

Sheikh Ibn Uthaimin (Rahimahullah) yace:

“Duk wanda bai yi wankan juma’ah ba ya aikata saɓon Allah, saboda Annabi (SAW) yace wajibi ne akan kowane baligi.” [Alliqah Ash-Shahri]

Annabi (SAW) yace:

“Duk wanda yayi wankan juma’ah zai kasance a cikin tsarki (daga laifukansa) har zuwa wata juma’ar.” [Sahihul Jami’u]

Shaqiq (Rahimahullah) ya kasance yana umurtar iyalan gidansa maza da mata (masu niyyar fita Sallar juma’ah) da yin wankan juma’ah.” [Almusannaf]

“Jinkirin zuwa juma’ah yana sabbaba jinkirin shiga Aljannah (koda kuwa mutum yana daga ma’abotan Aljannar).” [Sahihul Jami’u]

Anas Bin Malik (Rahimahullah) yace:

“Mun kasance muna sammakon zuwa Sallar juma’ah, kuma muna yin (bacci) ƙailula bayan Sallar juma’ah.” [Sahihul Bukhari]

Annabi (SAW) yace:

“Duk wanda yayi sammakon zuwa masallacin juma’ah a sa’a ta daya yana da ladar yin sadaka da rakumi. a sa’a ta biyu yana da ladar yin sadaka da Saniya. a sa’a ta uku yana da ladar yin sadaka da rago. a sa’a ta hudu yana da ladar yin sadaka da kaza. A sa’a ta biyar yana da ladar yin sadaka da kwai.” [Bukhari da Muslim]

Ibn Uthaimin (Rahimahullah) yace:

“Yawan tsawaita huɗubah (ranar Juma’ah) yana sanya mutane gajiya da kyamatar wa’azi.” [Nurun Alad-Darb]

Annabi (SAW) yace:

“A ranar Juma’ah mala’iku suna tsayawa a ƙofofin masallaci, suna rubuta masu shigowa, idan liman ya iso sai su naɗe takardun su saurari huɗubar liman.” [Sahihul Bukhari]

Annabi (SAW) yace:

“Yana daga Sunnah, fuskantar liman (wato kallonsa) yayin huɗuɓah ranar juma’ah.” [As-Sahihah]

“Amsa sallama da amsawa mai atishawa baya inganta a yayin da limami yake hudubar juma’ah.” [Fatawa Lajnatid-Da’imah]

“Ya tabbata a Shari’ah, cewa ana yin Sallar nafilah raka’ah biyu bayan juma’ah.” [Bukhari da Muslim], “ko raka’ah hudu.” [Muslim]

Imam Ibn Al-Qayyim (Rahimahullah) yace:

“Mai niyyar yin nafilarsa ta bayan jumu’ah a masallaci zai yi raka’ah hudu ne (biyu sau biyu), idan kuma a gida ne sai yayi raka’ah biyu.” [Zadul Ma’ad]

Imam Ibn Rajab Al-hambali (Rahimahullah) yace:

“Kamar yadda Sallar dare ta ke zama sanadiyyar kankarar zunubban bawa, haka ta ke sanya ɗaukakar darajar sa.” [Lada’iful Ma’arif]

Imam Fudail Bin Iyad (Rahimahullah) yace:

“Zama a majalisin ilimi ta hanyar tausayawa da kyautata mu’amala yafi Sallar dare da azumin yini.” [Wafayatul A’yan]

Annabi (SAW) yace:

“Kada (ka sake) ka tuhumi Allah akan abinda ya zartar na ƙaddara a kan ka.” [As-Sahihah]

Imam Ubaid Bin Umair (Rahimahullah) yace:

“Ba rashin haƙuri ne zubar da hawaye ko nuna damuwa a zuciya ba, rashin haƙuri shine munana lafazi da munana zato ga Allah.” [Uddatus-Sabirin]

Umar (RA) yace:

“Babu alkhairin da Allah yayi wa mutum bayan Musulunci sama da samun ɗan’uwa (ko aboki) na kirki.” [Qutul-Qulub]

Sheikh Bin Baz (Rahimahullah) yace:

“Ana lissafa wadanda suka mutu a hatsarin mota a matsayin shahidai, saboda mutuwarsu tana kama da waɗanda gini ya ruguzo masu.” [Nurun Alad-Darb]

Sheikh Ibn Uthaimin (Rahimahullah) yace:

“Yanayin tunanin mutum yana da tasiri sosai a kan sa (Kamar yadda baban mu, marigayi Alhaji Bashir Tofah, Allah ya gafarta masa, ya sanya wa wani littafinsa suna: tunaninka kamanninka), mutum na iya tunanin rashin lafiya alhali lafiyarsa kalau kuma rashin lafiya ya kama shi. Ko kuma mutum yayi tunanin lafiyarsa kalau alhali baya da lafiya, kuma rashin lafiyar ta tafi daga gare shi, ya samu sauki.” [Alqaulul-Mufid]

Sheikh Ibn Uthaimin (Rahimahullah) yace:

“Ba ya halatta ga mace (wadda sabubba da dalilai da hujjojin aurenta suka cika) ta hana kanta ko a hana ta yin aure, akan dalili ko hujjar sai ta kammala karatun jami’ah.” [Alliqah Ash-Shahri]

Ibn Mas’ud (RA) yace:

“Ado da mace take yi iri biyu ne, na fili (da kowa ke iya ganinta dashi, tufafin ta) da na ɓoye (ga mijinta kaɗai).” [Musannaf]

Ibn Mas’ud (RA) yace:

“Yana daga adon mace na ɓoye da ya keɓanci mijinta, idanun da suka sha ado/kwalli (ko leɓɓa masu janbaki), hannu mai ado da warwaro da zobe.” [Musannaf]

Imam An-Nawawi (Rahimahullah) yace:

“Makaruhi ne tsinke gashin furfura (daga kai ko gemu).”

Imam Muqbil (Rahimahullah) yace:

“Idan liman yana cikin khuɗubar juma’ah, sai alwalarsa ta warware, to zai cigaba da khudubah har sai ya gama; mamu su jira shi, ya sake alwala don yayi masu Sallah.”

Huzaifah Bin Qatadah (Rahimahullah) yace:

“Idan kayi wa Allah ɗa’a (biyayya) a sirri (wato a ɓoye), to Allah zai shiryar da zuciyarka, ko kaƙi ko kaso.” [Sifatu-Safwah]

Imam Sufyanuth-Thawri (Rahimahullah) yace:

“Lallai ne akan mutum ya tilasta wa ɗansa yin ilimi (na addini), saboda shi (uban) abin tambaya ne akan hakan gobe Alkiyamah.” [Siyaru A’lamin-Nubalah]

Imam Ibn Al-Qayyim (Rahimahullah) yace:

“Idan zuciya ta samu haske (na imani), to tawagar alkhairi na bibiyarsa daga kowace nahiya.” [Jawabul-Kafi)

Sheikh Nasirudin Al-Albani (Rahimahullah) yace:

“Aske gemu haramun ne, wannan kuwa da ittifaƙin mazhabobi guda huɗu (shahararru).” [Mutafarrighatush Sharid]

Imam Ibn Al-Qayyim (Rahimahullah) yace:

“Ita godiya (kamar sojan kariya ne) na ni’imah, daga dukkan abinda zai sabbaba gushewarta.” [Bada’iul Fawa’id]

Imam Mujahid Bin Jabr (Rahimahullah) yace:

“Kame gani daga abubuwan haramun suna sabbaba ƙaunar Allah (kishiyar hakan kuma yana sabbaba ƙiyayyarsa).”

Sheikh Ibn Uthaimin (Rahimahullah) yace:

“Sallah ita ce sanyin idon mumini, kuma guzurinsa na (kowane) yini don haɗuwa da ubangijinsa.” [Makarimil Akhlaq]

Annabi (SAW) yace:

“Littafin Allah (AlKur’ani) shine igiyar Allah da aka zuro daga sama zuwa doron ƙasa.” [Sahihul Jami’u]

Sheikh Al-Allamatus-si’idi (Rahimahullah) yace:

“Yana daga (abubuwa) mafi kuɓutarwa daga azabar wuta, kyautatawa halittun Allah da dukiya da kuma zance.”

Imam Fudail Bin iyad (Rahimahullah) yace:

“Ina tausayawa mutane uku: 1. Mai mulkin da ya ƙasƙanta; 2. Mai arziƙin da ya talauce; 3. Malamin da duniya ke wasa da shi.” [Siyaru A’lamin-Nubalah]

Wassalamu Alaikum,

Daga Dan uwanku: Imam Murtadha Muhammad Gusau, Okene, Jihar Kogi ~ 08038289761.

Tags: AbujaIslamLabaraiNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

Kotu ta tsare magidanci da ya yi lalata da yarinya ta dubura a kurkukun kirikiri

Next Post

KWATAGWANGWAMAR 2007: ‘Da na ga dama da na yi tazarcen zango na uku, saboda na san kitimirmirar da zan ƙulla na, amma ban yi hakan ba – Obasanjo

Next Post
KWATAGWANGWAMAR 2007: ‘Da na ga dama da na yi tazarcen zango na uku, saboda na san kitimirmirar da zan ƙulla na, amma ban yi hakan ba – Obasanjo

KWATAGWANGWAMAR 2007: 'Da na ga dama da na yi tazarcen zango na uku, saboda na san kitimirmirar da zan ƙulla na, amma ban yi hakan ba - Obasanjo

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • CUTAR DIPHTHERIA: Abubuwa 9 da ya kamata a sani game da cutar
  • GIRGIZAR KASA TA GIRGIZA DUNIYA: Ta ci rayukan mutum kusan 5,000 a Siriya da Turkiyya
  • INEC ta fara horas da ma’aikata 1,265,227, waɗanda za su yi aikin zaɓen 2023 – Okoye
  • Kotu ta bada umarnin a garƙame Shugaban EFCC, Bawa a kurkuku
  • DAINA AMFANI DA TSOFFIN KUƊI: Kotu ta umarci CBN kada ya wuce wa’adin 10 Ga Fabrairu

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.