Na daɗe ina sauraren mutane musamman mazauna yankin Kaduna ta tsakiya, akan inda takaddamar wanene asalin ɗan takarar kujerar Sanata na Kaduna ta tsakiya ya ki ci ya ki cinyewa, ko yaya za ta kaya a takarar wannan kujera daga karshe, Oho.
Har yanzu dai mutane da dama na ganin Lawal Adamu, Mr La ne ya fi dacewa yayi takarar kujerar, sai dai kuma bayan akasi da aka samu a wajen zaɓen Fidda gwani na jam’iyyar kotu ta soke zaɓen sannan ta ba jam’iyyar dama ta sake zaɓen fidda gwani. Kamar yadda muka ji wai an yi zaɓen sai dai kuma Mr La bai yi takarar ba. Ya ce maganan matsalar zaɓen fidda gwanin na gaban kotu saboda haka ba zai shiga zaɓen ba.
Amma kuma mu mazauna cikin garin Kaduna wani abu daban muke ji. An ce dagangar ne aka soke zaɓen don kawai domin dan takarar APC, Mohammed Sani Dattijo ya yi nasara a zaɓen. A cewar masu hasashe da fashin baki a siyasar Kaduna sun ce Sardaunan Badarawa ba da gaske yake yi ba ya na gyara wa APC hanya ne domin su yi nasara.
Ni dai ban ga alamun haka ba domin na ga kamar Usman Ibrahim, Sardaunan Badarawa da gaske ya ke yi. Ya tunkari Kamfen gadan gadan a cikin kwanakin nan. Sai dai duk da haka duk inda ka tada maganar sa a tsakanin mutane za ka ji ana cewa wai duk bula ce, da gangar aka dafa masa don ya kada Mr La ya zama ɗan takara don APC ta yi nasara, wato Dattijo ya yi nasara a zaɓen shiyyar.
Idan ma haka ne, to lallai kam zan iya cewa zai lalata siyasar sa tun da asubar farko kenan domin haka mutane ke ta zargi. Sannan kuma a nasu ɓangaren, wato ɓangaren APC, ba su nuna akwai matsala da nasarar da Sardaunan Badarawa ya samu a zaɓen fidda gwanin ba. Hasali ma an ji su sun rage kururuwa ne, kamar dai faɗuwa ce ta zo daidai da zama.
Ba a san maci tuwo ba sai miya ta ƙare, yanzu dai da ni da mai karatu da sauran ƴan jihar Kaduna ta tsakiya duk zamu zuba ido ne mugani ko da gaske ne ko kuma ma dai koma meye. Yar fara zata nuna. Amma a ganina, kada Dattijo, a siyasar Kaduna ta tsakiya ba a nan kusa ba. Lokaci kawai muke jira.
Ramatu Sarki, Malama ce mai yin sharhi da nazarin siyasa mazauniyar jihar Kaduna
Discussion about this post