‘Yan bindiga sun kashe mutum biyu a cocin Celestial dake kauyen Felele kusa da Lokoja a jihar Kogi ranar Lahadin da ta gabata.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar William Aya wanda ya sanar da haka wa manema labari ya ce mutum uku sun ji rauni a dalilin wannan harin.
Aya ya ce maharan sun dira wannan coci ne inda suka yi kan mai uwa dawabi da bindigogi, suna ta harbe harbe.
Ya ce kwamishinan ‘yan sandan jihar da mataimakin kwamishinan jihar duk sun bada umurin gudanar da bincike domin gano da kamo wadannan mahara da suka aikata wannan mummunar abu.
Bayan haka Wata kungiyar rajin kare hakkin dan Adam ‘Human Rights Writers Association of Nigeria HURIWA’ ta yi tir da harin kuma ta yi kira ga gwamnati da ta samar da tsaro a jihar.
Kungiyar ta ce rashin tsaro na gab da zama ruwan dare a jihar Kogi yanzu a dalilin rashin mai da hankalin gwamnati wajen samar da tsaro a jihar.
Idan ba a manta ba a manta ba a watan Agustan 2021 ‘yan bindiga sun yi garkuwa da mutum uku a cocin ‘Living Faith Church’ dake kauyen Osara a karamar hukumar Adavi.
Kuma a Satumbar 2021 ‘yan bindiga sun kashe mutum daya suka yi garkuwa da mutum biyu a cocin ECWA dake hanyar Kabba zuwa Okene.
Discussion about this post