Hedikwatar tsaron ƙasa DHQ ta bayyana cewa rundunar ‘Operation Hadin Kai’ ta ci gaba da samun nasarori a yaki da Boko Haram da ‘yan bindiga inda a cikin makonni biyu da suka wuce ‘yan ta’adda 466 sun mika wuya.
Darektan yada labarai na hukumar manjo-janar Bernard Onyeuko ya sanar da haka da yake bayanin aiyukkan da dakarun suka yi daga ranar 10 zuwa 24 ga Fabrairu ranar a Abuja.
Onyeuko ya ce ruwan bamabaman da sojin sama da na ƙasa suka yi ya taimaka wajen sadaukar da kai da ‘yan ta’adda 466 suka yi suka mika wuya. Cikin su akwai maza 120, mata 137 da yara 209.
Bayan haka Onyeuko ya ce ruwan bama-baman da rundunar sojin sama ta yi ranar 11 ga Fabrairu a Marte jihar Borno ya kashe wani shahararren dan bindiga Muhammed Yusuf da wasu yaran sa.
“Dakarun sun kashe ‘yan bindiga 10, sun kama 26 sannan sun kwato makamai da motocin bindiga guda hudu.
“Sannan an ceto mutum 20 da ‘yan bindigan suka yi garkuwa da su.
Daga nan rundunar ‘Operation Hadarin Daji’ sun kashe wani shahararren dan bindiga Dogo Umaru a dajin yankin jihar Zamfara.
Onyeuko ya ce rundunar ta yi nasarar kashe ‘yan bindiga 10, an kama makamaida dabobbin da aka sace sannan an ceto mutum 10 da aka yi garkuwa da su.
Onyeuko ya ce rundunar ta yi nasarar sasanta kabilun matasan Irigwe da Fulani domin Samar da zaman lafiya a yankin ranar 17 ga Febrairu.
Sannan kuma rundunar ‘Operation Whirl Stroke’ ta gama da ‘yan bindiga sama da 75 a Birnin Gwari jihar Kaduna.
Onyeuko ya ce rundunar ta kashe ‘yan bindiga biyar kuma an ceto mutane da dama da aka yi garkuwa da su a jihar Benue.
Ya jinjina namijin kokarin da dakarun sojojin suka yi sannan ya yi kira ga mutane da su rika hada hannu da jami’an tsaro domin kawar da rashin tsaro a kasar nan.
Discussion about this post