Hukumar dakile yaduwar cututtuka ta ƙasa NCDC ta bayyana cewa daga ranar daya zuwa bakwai ga Nuwanba mutum hudu sun mutu a dalilin kamuwa da cutar Kwalera.
Hukumar ta ce an samu mutum 78 wanda ake zaton sun kamu da cutar daga jihohi shida a kasar nan.
Wadannan jihohi sun hada da Barno, Kebbi, Adamawa, Oyo, Ogun da Rivers.
Duk da haka hukumar ta ce an samu ragowa yaduwar cutar a mako na 44 da mako na 43 Wanda aka samu mutum 409.
Zuwa yanzu cutar ta kashe mutum 3,449 sannan ana zargin mutum 100,057 sun kamu da cutar a kasar nan.
Idan ba a manta ba a watan Nuwanba PREMIUMTIMES HAUSA ta buga labarin cewa mutum 417 sun kamu sannan mutum 21 sun mutu a jihohi bakwai a kasar nan.
Hukumar ta ce an samu karin ne tsakain ranar 11 zuwa 17 ga Oktoba 2021.
Daga watan Janairu zuwa ranar 17 ga Oktoba cutar ta yi ajalin mutum 3,283 sannan hukumar ta ce akwai mutum 93,362 da ke dauke da cutar a jihohi 36 da Abuja.
Ga abubuwa 10 dake haddasa barkewar cutar a kasar nan
1. Rashin tsafta da barin ƙazanta a gida, musamman abinci da kayan abinci ko kwanukan cin abinci.
2. Zubar da tulin shara da bola aikin unguwanni, wadda ruwan sama ke maida ƙazantar ta s cikin jama’a.
3. Zubar da shara ko bola ko bayan gida a cikin ƙaramu da magudanan ruwa.
4. Yin bayan gida a fili ko a kan bola.
5. Rashin ruwa mai tsafta a cikin al’umma.
6. Ƙarancin asibitocin kula da marasa lafiya a cikin jama’a marasa galihu.
7. Ƙaranci ko rashin magungunan da za a bai wa mai cutar kwalara cikin gaggawa.
8. Matsalar ƙarancin jami’an kiwon lafiya a cikin jama’a.
9. Rashin hanyoyi masu kyau da za a garzaya asibiti da mai cutar amai da gudawa cikin gaggawa.
10. Shan ruwan ƙarama ko kogi, wanda ake zubar da shara, kashin dabbobi da kuma bayan gida.