Gwamna Nasir El-Rufai na Jihar Kaduna, ya aika da saƙon ta’aziyya da jimami ga iyalan waɗanda ‘yan bindiga suka kashe da waɗanda suka sace a Kudancin Kaduna, cikin yankin Chikun da Ƙaramar Hukumar Igabi.
Cikin wata sanarwa da Kwamishinan Harkokin Tsarin Cikin Gida Samuel Aruwan ya fitar a ranar Litinin, ya ce jami’an tsaro sun bada rahotonnin yadda ‘yan bindiga suka kai hari a Cocin Baftisma na Emmanuel a garin Kakkau Daji da ke cikin Ƙaramar Hukumar Chikun, har suka kashe Yusuf Dauda a cocin.
Sannan kuma maharan sun kwashi mutane da dama suka yi gaba da su a cikin daji.
Sanarwar da Aruwan ya fitar ta tabbatar da an ji wa wani mai suna Musu Yusuf rauni a cocin.
“Kuma ‘yan bindiga sun kashe wani mai suna Ɗahiru Sani a Kangon Kadi duk dai a cikin Ƙaramar Hukumar Chikun da wani Bello Alhaji a cikin Ƙaramar Hukumar Igabi, a wani ƙauye mai suna Barebari.
“Har yau a wannan yanki a garin Sauran Giwa, an kashe Hakilu Umar da Muntari Umar, a lokacin da su ke kan hanyar komawa gida daga wurin ibadar su.
“Gwamna El-Rufai ya yi addu’ar neman rahama ga mamatan tare da kira ga jami’an tsaro su ƙara zage damtse.”
Mutum 100 Aka Gudu Da Su A Cocin Baftisma -CAN:
Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya Reshen Jihar Kaduna, ta ce an yi garkuwa da mutum 100 a harin da ‘yan bindiga suka kai a Cocin Baftisma na Emmanuel ɗin.
Shugaban CAN na Jihar Kaduna, Hayeb, ya ce gaskiya babu wani ƙarin matakan tsaron da ake samu a yankin a duk lokacin da gwamnati ta sha masu alwashin inganta tsaron.
Kakkau Daji dai ya na kusan kilomita uku tsakanin garin da Sabon Tasha.
Ya kuma yi kukan cewa kulle layukan wayoyin da aka yi ba su inganta tsaro a yankunan ba, sai ma ƙara taɓarɓarewar da matsalar tsaron ta yi.
“Kulle layukan waya ya sa waɗanda aka yi garkuwa da su sun kasa kiran jama’a domin a kai masu gudunmawa.” Inji CAN.
Discussion about this post