• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Yadda sojoji suka cafke gogarman masu garkuwa da mutane da wasu 150 a dazukan Zamfara da Katsina

    Askarawan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 42, sun kama 20 sannan sun ceto mutum 63 da aka yi garkuwa da su – DHQ

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Crisis in Jos

    BAUCHI: Matasa sun babbake gidaje da shaguna da dama a Warji bayan Rhoda Jatau ta yi kalaman ɓatanci ga Annabi SAW

    GUDUN YIN BIYU-BABU: Gwamnan Bauchi ya sayi fam ɗin sake yin takarar gwamna, daidai lokacin da ya fito takarar shugaban ƙasa a PDP

    Farin jinin Buhari da mara min baya da yayi ya sa na samu daukaka a siyasa – Bala Mohammed

    Kano State Assembly

    Dan majalisar dokoki na jihar Kano ya doka ‘Ribas’ bayan ya tsunduma lambun jam’iyyar NNPP, ya ya rungumi tsintsiyar sa ya dawo APC

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Dalilin da ya sa Buhari ya dakatar da Akanta Janar ɗin da ake zargi da kantara satar naira biliyan 80

    Nigerian Pilgrims

    HAJJIN BANA: Duk wanda ya zarce shekaru 65 bashi ba Hajji bana – Hukumar Alhazai

    Beggars

    Almajirai da mabarata sun kwararo Abuja – Mahukunta

    HARƘALLAR KWANGILA: EFCC ta kama Patricia Etteh, tsohuwar Kakakin Majalisar Tarayya

    HARƘALLAR KWANGILA: EFCC ta kama Patricia Etteh, tsohuwar Kakakin Majalisar Tarayya

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Yadda sojoji suka cafke gogarman masu garkuwa da mutane da wasu 150 a dazukan Zamfara da Katsina

    Askarawan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 42, sun kama 20 sannan sun ceto mutum 63 da aka yi garkuwa da su – DHQ

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Crisis in Jos

    BAUCHI: Matasa sun babbake gidaje da shaguna da dama a Warji bayan Rhoda Jatau ta yi kalaman ɓatanci ga Annabi SAW

    GUDUN YIN BIYU-BABU: Gwamnan Bauchi ya sayi fam ɗin sake yin takarar gwamna, daidai lokacin da ya fito takarar shugaban ƙasa a PDP

    Farin jinin Buhari da mara min baya da yayi ya sa na samu daukaka a siyasa – Bala Mohammed

    Kano State Assembly

    Dan majalisar dokoki na jihar Kano ya doka ‘Ribas’ bayan ya tsunduma lambun jam’iyyar NNPP, ya ya rungumi tsintsiyar sa ya dawo APC

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Dalilin da ya sa Buhari ya dakatar da Akanta Janar ɗin da ake zargi da kantara satar naira biliyan 80

    Nigerian Pilgrims

    HAJJIN BANA: Duk wanda ya zarce shekaru 65 bashi ba Hajji bana – Hukumar Alhazai

    Beggars

    Almajirai da mabarata sun kwararo Abuja – Mahukunta

    HARƘALLAR KWANGILA: EFCC ta kama Patricia Etteh, tsohuwar Kakakin Majalisar Tarayya

    HARƘALLAR KWANGILA: EFCC ta kama Patricia Etteh, tsohuwar Kakakin Majalisar Tarayya

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Yadda watsi da asibitin biliyoyin naira da gwamnatin Jigawa ta yi ya jefa al’ummar jihar cikin ha’ula’i

Abubakar MaishanubyAbubakar Maishanu
July 7, 2021
in Babban Labari, Rahotanni
0
Yadda watsi da asibitin biliyoyin naira da gwamnatin Jigawa ta yi ya jefa al’ummar jihar cikin ha’ula’i

Gwamnatin jihar Jigawa ta yi watsi da aikin ginin wani asibiti mai gado 250 da aka fara shi a ƙaramar hukumar Hadejia, shekaru biyar (5) da su ka wuce.

Tun da farko an baiwa kamfanin Philko kwangilar aikin ginin asibitin ne akan kuɗi kuɗi Naira Biliyan Ɗaya da Miliyan Ɗari Biyar, daga bisani aka sake duba kuɗin kwangilar inda aka mayar da ita Naira Biliyan Ɗaya da Miliyan Ɗari Takwas, kamar yadda daraktan bin diddigin ayyuka da gudanar da shi akan daidaitacciyar hanya na jihar Jigawa, Ado Husseini ya bayyana.

Menene Tarihin Kwangilar Ginin Asibitin?

An tsara aikin samar da asibitin ne da nufin ya zama asibiti mafi girma a masarautar Hadejia, wanda zai maye gurbin tsohon asibitin da firimiyan jihar Arewa marigayi Sa Ahmadu Bello ya gina shi a shekarar 1962.

Masarautar ta Hadejia ta ƙunshi ƙananan hukumomi guda takwas da su ka haɗa da ƙaramar hukumar Hadejia da Mallam Madori da Kaugama da Auyo da Kafin Hausa. Sauran sun haɗa da Kirikassamma da Birnawa da kuma Guri.

Tun da farko Gwamna Muhammad Badaru ya ƙaddamar da shirin kwangilar ginin asibitin ne a ranar 27 ga watan Disambar shekarar 2017, inda aka baiwa kamfanin Philko kwangilar akan kuɗi Naira Biliyan Ɗaya da Miliyan Ɗari Biyar, tare da baiwa kamfanin wa’adin watanni 18 wajen kammalawa.

A lokacin bikin ƙaddamarwar an jiyo Gwamna Badaru yana cewa “Za a gina wannan asibitin a cikin watanni 18 kacal, kuma kamfanin gine – gine na Philko ne ya samu nasarar samun kwangilar ginin asibitin bayan ya cika dukkanin wata ka’ida”

Ya ƙara da cewa “Wannan aikin shi ne irinsa na farko a faɗin jihar Jigawa, kuma hatta maƙotan jihohin irinsu Yobe da Bauchi da ma jamhuriyar Nijar za su amfana da asibitin idan aka kammala shi”

Haka kuma a gurin taron mai martaba Sarkin Hadejia, Abubakar Maje – Haruna ya bayyana farin cikinsa bisa kawo ginin asibitin zuwa masarautar sa. Ya ƙara da cewa “Wannan aiki da shi ne irinsa na farko da al’ummar masarautar Hadejia su ka shafe gomman shekaru suna mafarkin tabbatar sa”

Shekaru Biyar Da Watsi Da Aikin Ginin Asibitin

A cikin shekarar 2021 jaridar PREMIUM TIMES ta bi diddigin yadda aka yi watsi da aikin ginin asibitin, inda ta gano har yanzu a nan jiya – i – yau duk da wa’adin da gwamnan ya bayar na kammalawa akan lokaci a shekarar 2019.

Haka kuma PREMIUM TIMES HAUSA ta bi diddigin kasafin kuɗin jihar Jigawa, inda ta gano tsahon shekaru ba a iya saka kuɗin aikin ginin asibitin na Hadejia tare da wasu asibitocin da ake ginawa a ƙananan hukumomin Birnin Kudu da Kazaure

A kasafin kuɗin shekarar 2017 an amince a kashewa gini asibitocin Naira Biliyan Ɗaya da Miliyan Ɗari Biyu, sai dai iya kuɗin da aka saka domin yin aikin su ne Naira 377,297,299. Inda aka yi amfani da kuɗin wajen kammala aikin babban asibitin Birnin Kudu da cigaba da aikin ginin asibitin na Hadejia da kuma sanya tubalin ginin asibitin kwararru da ke Kazaure.

Haka kuma a kasafin kudin shekarar 2018 an ware Naira Miliyan 600 domin cigaba da aikin asibitin sai dai an fitar da Naira 745 997,586. Haka kuma a shekarar 2018 gwamnatin jihar ta kashe kuɗin da ya zargi wanda aka ƙayyade a kasafin kudin, inda ta kashe Naira 145,997,586, sai dai babu tabbacin ko majalisar dokokin jihar wacce ta ke ƴar amshin shatar gwamanatin jihar ta amince da fitar da kuɗin.

A kasafin kuɗin shekarar 2019, an ware kuɗin fiye da Naira Biliyan Ɗaya da Miliyan Ɗari Biyar domin ginin asibitoci uku, sai dai iya Naira 1, 380,170,420 aka fitar.

Hakazalika a ƙunshin bayanan kasafin kudin shekarar 2020 ya nuna cewa an warewa aikin ginin asibitin na Hadejia Naira miliyan 574. Sai dai a kasafin kuɗin shekarar 2021 an ware Naira Biliyan Ɗaya da Miliyan Ɗari Uku akan aikin ginin asibitoci uku. A cikin kuɗin har da aikin kashi na biyu na asibitocin.

Sai dai kamar lokutan baya, a yanzu abu ne mai wahala mutum ya samu cikakken bayani ko kuma bibiyar yadda tsarin kasafin kuɗin jihar ta Jigawa ya ke, wanda hakan ne zai sanya a yiwa gwannatin adalci kamar yadda wani ɗan jarida Ahmad Rufa’i ya bayyana.

“A mulkin soja kwamishinan kuɗi ne ke tara ƴan jarida da manema labarai ya yi musu bayanin abubuwan da kasafin ƙudi ya kunsa, amma shekaru shida a wannan gwamnatin an yi watsi da wannan ɗabi’ar wanda hakan ya kara ɗabi’ar cin hanci da rashawa” in ji ɗan jaridar.

Dan jaridar ya ƙara da cewa kamata ya yi gwamnati ta dinga gudanar da ayyukanta a buɗe ta yadda hakan zai gina gaskiya tsakanin waɗanda ake mulka da kuma shugabanni, kuma hakan ne zai sanya al’umma su gamsu cewa ana tafiyar da dukiyarsu ta hanyar da ya kamata.

Me Al’ummar Masarautar Hadejia Su Ke Cewa?

Shugaban ƙungiyar cigaban masarautar Hadejia wato Hadejia Emirate Development Association, (HEDA) Abdullahi Kafinta, ya ce sun rubuta ƙorafi akan yadda ɗan Kwangilar ke jan ƙafa akan aikin ginin asibitin tare da miƙa ƙorafinsu zuwa ga mutanen da abin ya shafa ciki har da Gwamna Muhammadu Badaru Abubakar, amma babu wani mataki da aka ɗauka.

Abdullahi Kafinta ya ce babu wani aiki da gwamnati za ta gudanar da shi a masarautar Hadejia ba tare da kungiyarsu ta HEDA ta bibiye shi ba, tare kuma da wayar da kan al’ummar masarautar akan alfanun sanya ido dan ganin aikin ya kammala.

Ya ƙara da cewa amma akan batun yadda aka yi watsi da ginin asibitin kwararru na Hadejia, babu wanda zamu zarga sai gwamnatin jihar domin ita ta bayar da wa’adi kuma wa’adin ya daɗe da wucewa kuma mun rubutawa gwamnatin ƙorafi daban – daban domin jin dalilin da ya sanya aka yi watsi da aikin, amma shiru babu amsa.
“Watsar da aikin ginin asibitin da gwamnatin jihar Jigawa ta yi yana damun mu domin idan mu kalli yadda wa’adin zangon mulkin gwamanatin na biyu ya ke ƙarewa, kuma babbar damuwar al’ummar masarautar Hadejia ita ce gwamnatin Badaru ta ƙare ba tare da an ƙarasa ginin asibitin ba” In Abdullahi Kafinta

Haka kuma Abdullahi Kafinta ya ƙara da cewa mun rubutawa gwamnatin jihar Jigawa ƙorafi har kashi uku domin jin dalilan da ya sanya aka yi watsi da ginin asibitin amma shiru ka ke ji wai Malam ya ce Shirwa, wanda hakan ne ya sanya al’ummar masarautar Hadejia yanke ƙauna akan aikin.

Ya ce sakamakon rashin asibitin ƙwararru a yankin masarautar ta Hadejia, ya tilastawa al’ummar yankin zuwa maƙotan jihohi kamar su Kano da Yobe domin neman lafiya. Ya ce asibitin da ake da shi na gwamnati a yanki shi ne wanda Firimiyan jihar Arewa, Sa Ahmadu Bello Sardaunan Sokoto ya gina a shekarar 1962, wanda kuma ya yiwa al’ummar yankin kaɗan.

“Samar da asibitin kwararrun yana da matuƙar muhimmanci sai dai bamu gamsu da yadda ake tafiyar da aikin ba, domin mun bi diddigin yadda ake aiwatar da wasu ayyukan a wasu yankunan kuma tuni an kammalasu mutane sun fara amfana, amma me ya sa namu ya zama saniyar ware?” In ji Abdullahi Kafinta.

Ya ƙara da cewa a zabukan shekarun 2015 da 2019 al’ummar masarautar Hadejia sune su ka fi kowacce al’ummar masarauta kaɗawa gwamna Muhammad Badaru ƙuri’a, sai dai shiru bamu ga alfanun haka ba, domin gwamnatin ta yi watsi da mu”

Yadda aka bada kwangilar

Babban daraktan hukumar bin diddigin ayyuka da gudanar da shi akan daidaitacciyar hanya na jihar Jigawa, Ado Husseini ya musanta cewa babu gaskiya akan batun cewa wai an baiwa kamfanin da bai cancanta ba kwangilar ginin asibitin, ya ce hakan siyasa ce kawai da kuma hamayya daga ƴan adawa.

Ado Husseini ya ce tsarin kwangila yana tafiya ne tare da amincewa akan abin da ya ke cikin kasafin kudi, sannan kuma sai an bibiyi yadda aikin zai kasance kafin a amince da aikin. Kuma kwangilar asibitin kwararru na Hadejia shi ma sai da aka bi wannan bai zama na daban ba.

Haka kuma daraktan ya ce ayyukan ofishin bin diddigin na jihar Jigawa a buɗe ya ke babu wata ƙumbiya – ƙumbiya ko rashin gaskiya a dukkanin wani aiki da su ke gudanarwa, kuma suna ƙoƙarin wajen ganin an kammala dukkanin wani aiki akan darajar kuɗin da aka bayar domin a samu nagarta da ingancin aikin.

Ya ƙara da cewa tuntuni ya kamata a ce an kammala aikin ginin asibitin kwararru na Hadejia tare da ƙaddamar da shi amma ofishinsa ne ya ɗauki alhakin jan ƙafar da aikin ginin ya ke yi. ” Ofishin bin diddigin ayyuka shi ne silar da aikin kwangilar ke jan ƙafa tare da tafiyar hawainiya”
Ya ƙara da cewa “Babban burinmu ne mu ga an kammala aikin wannan asibiti tuntuni to sai dai an samu chanje – chanje a kwangilar ginin asibitin, domin da farko dai an sake fasalin taswirar ginin asibitin da kuma ƙoƙarin banbance gurin da aikin ginin asibitin zai dace, la’akari da irin yanayin ƙasar Hadejia”

“Da farko an bayar da kwangilar ginin asibitin ne akan kuɗi Naira Biliyan Ɗaya da Miliyan Ɗari Biyar, sai dai daga baya an sake duba fasalin kwangilar inda aka mayar da ita zuwa Naira Biliyan Ɗaya da Miliyan Ɗari Takwas, da nufin kammala kashin farko na ginin asibitin, kuma na tabbata yanzu haka an kammala aikin” In ji Ado Husseini.

Haka kuma babban daraktan ya ce wakilin da zai sanya daga ma’aikatar lafiya ta jihar Kano, ya rubutawa ɗan kwangilar takarda inda ya bayyana damuwarsa akan yadda aka samu jan ƙafa wajen aikin. Ɗan kwangilar ya buƙaci a ƙara masa watanni biyar, amma duk da haka ya gaza gabatarwa da ma’aikatar lafiyar fasalin aikin duk da ƙarin watanni da ya buƙata kuma aka ba shi”

Amma a yanzun nan da mu ke magana da kai (Alhamis 27 ga watan Mayu), ofishin bin diddigin aikin ya rubutawa ɗan kwangilar takardar akan ya dawo bakin aikin.

Dalilan Da Ya Sanya Ba Zamu Soke Kwangilar Ba

Ado Husseini ya ce babban dalilin da ya sanya gwamnati ba za ta soke kwangilar ba shi ne ba zai taɓa amfanar da ɓangarorin biyu, kuma akwai buƙatar al’ummar masarautar ta Hadejia su ƙara haƙuri.

Soke kwangilar zai mayar da hannun agogo baya, domin za a ɗauki tsahon shekaru ba tare da an kammala aikin kuma an ƙaddamar da shi ba daga ɓangaren gwamnati ba. A dan haka dukkanin wanda abin ya shafa da su yi haƙuri akan lamarin.

Ɗan Kwangilar Ba Ya Binmu Bashi
Shugaban hukumar bin diddigin ayyukan na jihar Jigawa, ya ce fiye da shekara guda gwamnatin jihar ta biya dukkanin wasu ƴan kwangila kudadensu, dan haka babu wani kamfani ko ɗan kwangila da ya ke bin gwamati ko Sisin Kwabo

“Na birgi kirji tare da tabbatar maka da cewa babu wani ɗan kwangila da ya ke bin jihar Jigawa ko Sisin Kwabo. Mun kammala dukkanin biyan kuɗaɗen ƴan kwangila ƙasa da wata. A game da wannan kwangilar kuma ta ginin asibitin kwararru na Hadejia ina tabbatar maka da cewa babu sauran wani kuɗi da ba a biya ɗan kwangilar ba” In ji Ado Husseini

Lamarin Ya Fusata Gwamna Badaru Har Yayi Barazanar Gayyato Hukumar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa Mai Zaman Kanta Ta ICPC A Cikin Lamarin

Wata majiya ta bayyana cewa batun aikin kwangilar ginin asibitin na Hadejia ya fusata Gwamna Badaru, lamarin da ya kai ga ya yi barazanar gayyato hukumar yaki da cin hanci da rashawa mai zaman kanta ta ƙasa ICPC, domin bincikar yadda aka yi watsi da kwangilar ta kasance.

Majiyar ta ƙara da cewa a maganar nan da mu ke da kai, Gwamna Badaru bai ji daɗin yadda aikin kwangilar ginin asibitin kwararru na Hadejia ba, musamman akan yadda su ka karya alkawari wanda hakan ya sanya ya samu ƙorafi daban-daban daga masarautar Hadejia, sai dai gwamnan ya gaza ɗaukar mataki sabdoa wanda aka danƙawa kwangilar abokin siyasar sa ne, wanda saboda wasu dalilai ba za a ambaci sunansa ba.

Hakazalika majiyar ta ce a ranar 7 ga watan Mayun shekarar nan, Gwamna Muhammad Badaru ya baiwa ofishin hukumar ICPC da ke Kano sabuwar Mota ƙirar Toyota Hilux, domin su samu karfin gwiwar bincikar yadda aikin kwangilar ya gudana.
A lokacin bayar da motar da gwamna Muhammad Badaru ya yi wanda ya samu wakilicin babban sakatare a ofishin sakataren gwamnatin jihar ta Jigawa, Ado Sadiq, ya bayyana cewa gwamnatin Jigawa, ta himmatu wajen yin koyi ga tsarin gwamnatin shugaba Muhammad Buhari, wajen ganin an bayar da dukkanin wata kwangila akan ka’ida da kuma doka da oda.

A nasa ɓangaren shugaban hukumar ta ICPC reshen jihar Kano, Umar Muhammad godewa gwamnan ya yi akan wannan gudummawar da ya baiwa ofishin na su, ya kuma sha alwashin yin amfani da motar yadda ya dace.

Ya ƙara da cewa hukumar ta ICPC za ta yi amfani da motar wajen bibiyar ayyukan da aka bayar a mazabu daban – daban da ke faɗin jihar.

Gwamnatin Jigawa Ta Himmatu Akan Aikin – Kakakin Gwamnati

Kwamishinan yaɗa labarai na jihar Jigawa, Malam Bala Ibrahim Mamsa ya bayyana jaridar PREMIUM TIMES, gwamnatin jihar Jigawa ta himmatu wajen ganin an kammala ginin asibitin ƙwararrun na Hadejia akan lokaci, ya kuma buƙaci al’ummar masarautar da su ƙara haƙuri akan batun.
Bala Ibrahim Mamsa ya ce asibitin na Hadejia yana cikin manyan cibiyoyin lafiya da gwamna Muhammad Badaru Abubakar ya mayar da hankali akai. Baya ga ginin asibitin na Hadejia, gwamnan ya yi alƙawarin gina karin wani asibitin a ƙaramar Kazaure ƙari kan na Hadejia.
Kwamishinan ya ƙara da cewa idan aka kammala ginin asibitin zai yi kafada da kafada da asibitin gwannatin tarayya da ke babban birnin jihar ta Jigawa.
“Muna tabbatarwa da al’ummar masarautar Hadejia cewa gwamnati ta himmatu wajen ganin an kammala aikin ginin asibitin ƙwararrun da ke yi” In Ji Bala Ibrahim Mamsa

Me Kamfanin Da Ya Ke Kwangilar Ya Ke Cewa Akan Batun?

Babban Injinyan da ke kula da aikin ginin asibitin Injiniya Habibu Aliyu da ya yi magana a madadin kamfanin na Philko ya shaidawa PREMIUM TIMES cewa babban dalilin da ya kawo tsaiko wajen aikin sun haɗa da yadda aka sake duba fasalin kwangilar da jinki wajen biyan kuɗi da kuma annobar cutar Korona da aka yi fama da ita.

“Bayan da kamfanin Philko ya buƙaci da a sake duba yanayin aikin kwangilar saboda yanayin ƙasar da za a yi aikin ba zai ɗauka ba, a nan ne gwamnati ta ɗauki tsahon watanni Takwai kafin ta bayar da amsa akan lamarin wanda hakan ne ya ƙara haifar da jinkirin aikin” In ji Habibu Aliyu
Injinya Habibu Aliyu ya ƙara da cewa wakilin ma’aikatar lafiya da zai sanya ido akan aikin bai sanar da gwamna Badaru cikakken bayani akan lamarin ba kuma haka ma a ɓangaren yadda aka sake duba fasalin kwangilar da kuma buƙatar biyan kuɗin sun ɗauki watanni uku (3) zuwa huɗu (4), wanda hakan ya sake haifar da jinkiri akan aikin.

A ƙarshe Injiniyan ya ce kamfanin na Philko zai iya kammala aikin ginin asibitin ne kawai idan har gwamnati ta sakar masa isassun kuɗi.

Tags: BadaruHadejiaHausaJigawaLabaraiNews
Previous Post

Yadda ‘ƴan bindiga suka maida nas-nas din da suka sace a Kaduna masu kula ‘yan uwan su da suka ji rauni

Next Post

Majalisar Katsina za ta maida gidajen kallo makarantun Islamiyya

Next Post
Majalisar Katsina za ta maida gidajen kallo makarantun Islamiyya

Majalisar Katsina za ta maida gidajen kallo makarantun Islamiyya

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • RASHIN TSARO: Ƴan bindiga sun kashe mutum 360 sun yi garkuwa da mutum 1,389 a jihar Kaduna cikin watanni uku
  • Askarawan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 42, sun kama 20 sannan sun ceto mutum 63 da aka yi garkuwa da su – DHQ
  • Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru
  • Yadda iyaye na su ka yi hijira zuwa Jihar Adamawa – Atiku Abubakar
  • BAUCHI: Matasa sun babbake gidaje da shaguna da dama a Warji bayan Rhoda Jatau ta yi kalaman ɓatanci ga Annabi SAW

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.