• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Zamfara ta zargin tsohon gwamna Matawalle da sace motocin gwamnatin jihar da wasu kayan gwamnati

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    Gwamnatin Kano ta rusa katafaren bene mai hawa uku da aka yi bisa filin gwamnati da Ganduje ya raba wa ƴan uwa da abokan arziki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TSAUTSAYI: Yadda ‘yan bindiga suka ware da Lami Awarware da Haulatu bayan halartar taron rantsar da Uba Sani a Kaduna

    Sojojin Najariya sun kara ragargaza wa Boko Haram motocin yaki bakwai

    Sojoji sun dagargaza matatun mai 47 sun kama barayin mai 65 – Hedikwatar tsaro na kasa

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    HAJJI 2023: Yadda jirgin maniyyatan Jigawa ya koma Kano ba shiri, bayan ya samu matsala cikin sararin samaniyar Kamaru

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

ANNOBAR KORONA. TSADAR ABINCI. KORAR MA’AIKATA. RASHIN TSARO. ZAFTARE ALBASHI: Yadda shan jar miya ya gagari talaka ko a mafarki

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
July 2, 2021
in Rahotanni
0
Mutum 9 cikin 10 a jihohin Sokoto, Taraba da Jigawa fakirai ne tuburan – Rahoton NBS

Abubakar Isma’il malamin firamare ne a Kano. Shi kuma Opeyemi Adeyemi ma’aikacin wani kamfani ne a Obalende, cikin Legas. Su biyun kukan su iri ɗaya dangane da masifar tsadar rayuwar da ake ciki.

“A wannan matsanancin halin, wanda aka rage wa albashi sai ya yi murna kawai, tunda ba korar sa aka yi ba ɗungurugun.

“To ni ba kora ta aka yi ba, albashi na aka zaftare. Wannan ibtila’i da ya same ni, ya canja rayuwa ta da ta iyali na. Saboda a yanzu haka abincin rana gagara ta ya ke yi, sai dai na riƙa ‘yan kame-kame.

“Ko dai na ci gasasshiya ko dafaffiyar masara da rana, na kwankwaɗi ruwa, ko kuma na jiƙa gari da ruwa da sukari na sha, na saurari jiran abincin dare.” Inji Adeyemi, wanda ya ƙara da cewa:

“Kuɗin wutar lantarki na neman gagara ta. Sauƙi na ma ba ni da yara ƙanana da yawa, amma da sai kuɗin makarantar yara sun gagare ni biya.”

Kamar Adeyemi kamar Isma’il, malamin firamaren da ya ce, “ai ni rabo na da sayen ƙaramin buhun shinkafa tun kafin Buhari ya hau mulki.”

Malamin ya ce a yanzu kafin ka ga gidan talakan da ake yin abinci da jar miya, sai wane-da-wane. Saboda kayan miya sun yi tsada kamar wasu kayan alfarma.”

Isma’il ya ce ba ya iya sayen kwanon wake saboda yanzu ya kai naira 1,600. Masara da gero da dawa waɗanda talaka ne ke noma su, a yanzu ko sunan su talaka ya ji wallahi sai hankalin sa ya tashi.”

Matsalar da Adeyemi da Ismail su ka shiga, irin ta ce miliyoyin ‘yan Najeriya da dama ke ciki a halin yanzu.

Bincike ya nuna a kullum kayan masarufi da kayan abinci su na tashi. Abin da ake sayarwa a kasuwannin birnin, ba daidai farashin sa yake da kasuwannin ƙauyuka masu ci sati-sati ba.

“Abin damuwar a kullum shi ne yadda farashin ke tashi a kowace kasuwanni. Abin da ka sani naira 500, idan ka koma wani sati naira 700 za a ce maka.”

Dalilan Tsadar Rayuwa Ga Talakan Najeriya:

Ɓullar cutar korona a ranar 27 Ga Janairu, 2020: Hakan ya tsayar da komai a ƙasar nan, ya karya tattalin arziki, miliyoyin ‘yan Najeriya sun talauce yayin da aka ƙaƙaba kullen korona.

Ƙarfin Tattalin Arzikin Cikin Gida Ya Samu Tawaya: Saboda masana’antu sun daina aiki. Babu kayan da ake sassafawa a cikin gida ana fitarwa a waje.

Sannan kuma masu aiki a masana’antu sun tagayyara, saboda an tilasta masu zaman gida.

Tarzomar #EndSARS: Wannan tarzoma ta haifar da kashe-kashe da asarar dukiyoyi masu ɗimbin yawa.

Dakatar da kai abinci a jihohin kudu da aka yi na wani lokaci ya haddasa masifar tsadar kayan abinci a kudancin ƙasar nan.

Matsalar Tsaro: Wannan babbar matsala ta haddasa tsadar rayuwa a Arewa, domin yankuna da dama noma ya gagara. Sannan kuma wasu kasuwannin yankunan karkara sun daina ci. Dama a irin waɗannan kasuwanni ake samun amfanin gona da arha, ana kaiwa cikin birane da garuruwa ana sayarwa.

Ƙarshen makon da ya gabata PREMIUM TIMES Hausa ta buga labarin yadda yadda buhun garin kwaki ya tsere wa talaka fintinkau.

Garin rogo, wanda a ƙasar Hausa aka fi sani da garin kwaki, ya na ɗaya daga cikin abincin da duk wanda a shekarun baya aka ga ya daddage ya na ƙasumar sa, to ana danganta shi da talauci ko ƙarancin wadatar aljihu ko ta abinci a gida.

Amma a yau, duk da ɗimbin kuɗaɗen da Gwamnatin Tarayya ke kashewa wajen bunƙasa noma, hakan bai hana garin kwaki fecewa a guje ba, ya bi sahun sauran kayan abincin da ake nomawa a gida wajen tsula tsadar tsiya.

Kamar yadda shinkafa, wake, masara, gero da dawa su ke neman su gagari talaka, tuni shi garin rogo ya shige gaban su wajen tsada. Ya tsere wa gero da dawa da masara. Kuma ya yi wa talaka fintinkau, sai gani sai hange daga nesa.

Buhun garin kwaki mai nauyin kilo 100, wanda a shekarun baya ake sayarwa naira 16,000, yanzu idan ba ka da naira 40,000 ba za ta ka iya sayen sa ba a jihohi irin su Cross River, inda ake ganin kamar can ne ma ya fi arha takyaf.

Binciken da PREMIUM TIMES ta gudanar ya nuna dalilai da dama da su ka haddasa ko da talaka ya iya sayen garin kwaki domin ya ci, to ba zai iya yi masa cin a ci a ƙoshi ba, irin wanda a shekarun baya ake tasa taiba a gaba ana ci har ciki ya cika.

Miliyoyin ma’aikatan da su ka ƙunshi na gwamnatin tarayya, jihohi da ƙananan hukumomi waɗanda albashin su bai kai naira 40,000 ba, ba su iya cin garin kwaki su ƙoshi su da iyalan su. Sai dai a yi cin daga-bana-sai-baɗi, wanda ake yi ranar da aka ɗauki albashi.

Maciya tuwon alabo, wanda ake yi da rogo, su ma yanzu sai gani sai hange, ba kowa ke iya buɗe ciki ya danƙari tuwon alabo ba, duk kuwa da sulɓin ta lomar tuwon ke da shi. Saboda ba ta da sulɓi a cikin aljihun talaka.

A Najeriya dai batun tsadar abinci kullum sai hauhawa ya ke yi, ya ƙi saukowa ko gsngarowa ko kuma mirginowa a ƙasa.

A ƙididdigar da Hukumar Ƙididigar Alƙaluman Bayanai ta Kasa ta yi a watan Afrilu, ta nuna cewa cikin watan Maris, 2021 kayan abinci a Najeriya sun yi tsadar da ba su taɓa yi a tsawon shekaru huɗu da su ka gabata ba.

Garin kwaki wanda shi ne aka fi nomawa na biyu daga masara a ƙasar nan, a yanzu bincike ya nuna wanda ake nomawa ɗin ba ya wadata.

Manoma irin su Grace Ebit da wasu masana sun danganta matsalar da rashin nahartaccen tsari da Gwamnatin Tarayya ke aiwatarwa, rashin kyakkyawan tsarin noma, rashin jari ko rashin lamuni daga gwamnati da kuma ƙarancin taki.

Masana sun ce kafin rogo ya sake yin arha a Najeriya, sai an dasa aƙalla metrik tan miliyan 28.3 a filin gonakin da aƙalla sun kai faɗin hekta miliyan 1.2.

Cikin watan Mayu PREMIUM TIMES HAUSA ta yi tsakuren yadda wake ya fi ƙarfin tukunyar girkin manoman da ke noma shi.

Tags: AbujaHausakoronaLabaraiNewsYunwa
Previous Post

Ba ni da ra’ayin takarar shugaban kasa, lokacin da aka zabe ni gwamnan Kaduna gashin kai na baki wul yanzu duk furfura – El-Rufai

Next Post

INGIZA MAI KANTU RUWA: Sunday Igboho ya ce a fita zanga-zanga Legas, amma shi ba zai samu damar halarta ba

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Ba mu son ganin ko Bafulatani ɗaya tal a yankin Yarabawa daga ranar litinin – Sunday Igboho

INGIZA MAI KANTU RUWA: Sunday Igboho ya ce a fita zanga-zanga Legas, amma shi ba zai samu damar halarta ba

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • ‘Ruhun Mai Tsarki ne ya umarce ni na kashe ta’ – Inji matar da ta kashe ‘yar shekara biyar
  • RIGA MALAM MASALLACI: Matasan Kano sun yi wa ginin ƴan canji diran mikiya, sun yi warwason kayan ‘ganima’
  • HIMMA DAI MATA MANOMA: Rashin jari mai kauri ya sa noma na ya ƙi gaba, ya ƙi baya – Wata mace mai himma
  • CIRE TALLAFIN MAI: Kungiyoyin ma’aikatan lantarki, Ƴan jarida da na Kwadago za su tsunduma yajin aiki daga ranar Laraba
  • Yadda bashin Dala Miliyan 19.3 na Bankin Musulunci ya bunƙasa noma a ƙananan hukumomin Kano 44 – Hamisu, Kodinetan KSADP

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.